Mar 23, 2019 06:00 UTC
  • New Zeland : Musulmi Sun Koma Ibada A Masallacin Christchurch

Musulmi a New Zeland, sun koma ibada a babban masallacin Christchurch, karon farko bayan mummunan harin ta'addancin da aka kai kan musulmin a ranar 15 ga watan Maris din nan.

Tagwayen hare haren bindigan wanda wani mai sassauran ra'ayi dan asalin kasar Austria ya kai a waccen Jum'ar data gabata ya yi sanadin shahadar musulmi 50.

Bayan hakan ne 'yan sandan yankin suka rufe masallacin domin gudanar da bincike da kuma tabbatar da tsaro.

'Yan sanda a kasar sun ce an kuma gudanar da gyara a gudan masallacin na biyu na  Linwood, inda dan ta'addan ya kashe mutane, saidai basu bayyana takamaimai ranar da za'a fara ibada a masallacin ba.

Saidai sun ce za'a karfafa matakan tsaro, ta hanyar jibge 'yan sanda a masallatan guda biyu, har sai abunda hali ya yi.

Tags