Jami'an Tsaro A Kasar saudiya Sun Kashe Mutane 5 A Yankin Watif
Jan 08, 2019 03:22 UTC
Mutane akalla 5 ne suka rasa rayukansu a kauyen Umm Al-Hamam na yakin Qatif a kasar Saudiya a lokacinda jami'an tsaron kasar suka kai sumame a kan mutanen kauyen.
Tashar Talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa jami'an tsaron kasar Saudiya sun kai sumame a kauyen Umm Al-Hamam na yankin Qatif ne a jiya Litinin, sannan sun kwashe sa'o'i 15 suna kawanya da kauyen. A lkacin ne suka yi ta kwasar kayakin mutanen kauyen a matsayin ganimar yaki. Mazauna yankin Qtif na kasar Saudiyya dai mabiya mazhabar Shi'a ne, kuma sun dade suna kokawa kan irin wariyar da ake nuna masu a gwamnatin masarautar Ali Sa'ud.
Tags