'Yan Sandan Myanmar Sun Tarwatsa 'Yan Buda Da Suka Kai Hari Kan Musulmi
https://parstoday.ir/ha/news/world-i20278-'yan_sandan_myanmar_sun_tarwatsa_'yan_buda_da_suka_kai_hari_kan_musulmi
Jmi'an 'yan sandan kasar Myanmar sun yi amfani da karfi wajen tarwatsa daruruwan 'yan addinin Buda da suka kai hari a kan musulmi.
(last modified 2018-08-22T07:00:05+00:00 )
May 11, 2017 07:28 UTC
  • 'Yan Sandan Myanmar Sun Tarwatsa 'Yan Buda Da Suka Kai Hari Kan Musulmi

Jmi'an 'yan sandan kasar Myanmar sun yi amfani da karfi wajen tarwatsa daruruwan 'yan addinin Buda da suka kai hari a kan musulmi.

Shafin yada labarai na Radionz cewa, a daren jiya mabiya addinin buda sun kaddamar da farmaki a kan musulmi a yankin Rangon, amma jami'an tsaro sun tsarwatsa su ta hanyar yin harbi a cikin isaka.

Maharan dai sun kai farmaki ne a kan makarantu da kuma masalatan musulmi, suna masu nuna rashin amincewarsu da duk wani aiki na ibada da musulmi za su gudanar a yankinsu, har sai sun biya haraji.