-
Khalid Abbud: Saudiyya Ta Bukaci Syria Da Ta Yanke Alaka Da Iran Da Hizbullah
Mar 27, 2018 17:22Sakataren majalisar dokokin kasar Syria Khalid Abbud ya bayyana cewa, wasu daga cikin kasashen larabawa da suka hada da Saudiyya da UAE, sun gabatar wa Syria tayin yanke alaka da Iran da kuma Hizbullah, bisa sharadin cewa idan Syria ta yi hakan, to su kuma za su daina taimaka ma 'yan ta'addan takfiriyya a kasar.
-
Sayyid Hasan Nasrullahi Ya Bukaci Kasashen Musulmi Da Su Nisanci Kulla Alaka Da H.K.Isra'ila
Jan 19, 2018 19:01Babban sakataren kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullahi da ke kasar Lebanon ya bukaci kasashen musulmi da su nisanci kulla alakar jakadanci da Haramtacciyar kasar Isra'ila.
-
Sayyid Nasrallah: Trump, "Isra'ila" Da Saudiyya Za Su Ji Kunya Kan Fatan Da Suke Da Shi Kan Rikicin Iran
Jan 04, 2018 05:47Shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon Sayyid Hasan Nasrallah ya bayyana cewar shugaban Amurka Donald Trump da kawayensa, na daga haramtacciyar kasar Isra'ila da Saudiyya za su ji kunya dangane da fatan da suke da shi kan rikicin baya-bayan nan da ya faru a Iran, kamar yadda kuma ya sake jaddada cewa matakin da Trump din ya dauka kan Kudus zai zamanto wani mafari da kawo karshen 'Isra'ila'.
-
Qudus : Matakin Trump, Ayyana Karshen Isra'ila Ne _ Nasrallah
Dec 11, 2017 16:08Shugaban Kungiyar Hezbollah ta kasar Labanon, Sayyid Hassan Nasrallah, ya bayyana cewa matakin Trump na Amurka kan ayyana Qudus babban birnin yahudawan sahayoniya 'yan mamaya shelanta kawo karshen Isra'ila ne.
-
Sayyid Hasan Nasrullah: Matakin Trump Tayar Da Sabuwar Fitina Ne
Dec 07, 2017 18:59Babban sakataren kungiyar Hezbollah ta kasar Labanon, ya mayar da martani dangane da matakin Donald Trump na ayyana birnin Qudus a matsayin babban birnin HK Israila.
-
Bayanin Babban Sakataren Kungiyar Hizbullahi Ta Kasar Lebanon Kan Makirce-Makircen Saudiyya
Nov 12, 2017 05:56Babban sakataren Kungiyar Hizbullahi ta kasar Lebanon ya fayyace irin tarin makirce-makircen da mahukuntan Saudiyya suke kitsawa kan kasar Lebanon musamman matakin da suka dauka na tilasta wa fira ministan kasar Sa'ad Hariri yin murabus daga kan mukaminsa.
-
Kungiyar Hizbullahi Ta Lebanon Ta Ce: Mahukuntan Saudiyya Ne Suka Tilastawa Sa'ad Hariri Yin Murabus
Nov 10, 2017 19:00Babban sakataren kungiyar Hizbullahi ta kasar Lebanon ya bayyana cewa: Mahukuntan Saudiyya ne suka tilastawa Sa'ad Hariri yin murabus daga kan mukaminsa na fira ministan Lebanon, kuma hakan babban cin mutunci ne ga fira ministan da ma dukkanin al'ummar Lebanon.
-
Sayyid Nasrallah: An Tilasta Wa Hariri Murabus Ne, Ba Bisa Son Ransa Ba
Nov 05, 2017 18:12Shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon Sayyid Hasan Nasrallah ya bayyana cewar an tilasta wa firayi ministan kasar, Sa'ad Hariri, yin murabus ne daga Saudiyya ba bisa son ransa ba, yana mai kiran al'ummar kasar da su kai zuciya nesa da kuma ci gaba da kokari wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankalin kasar.
-
Sayyid Nasrallah: Amurka Ce Take Hana Yakar Da'esh/Saudiyya Ce Tushen Fitina A Yankin G/Tsakiya
Oct 08, 2017 17:04Shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon Sayyid Hasan Nasrallah ya bayyana cewar Amurka ce take hana kokarin da ake yi na ganin karshen kungiyar ta'addancin nan ta Daesh, kamar yadda kuma Saudiyya da H.K.Isra'ila su ne ummul aba'isin din rashin tsaron da ake fuskanta a yankin Gabas ta tsakiya.
-
Sayyid Nasrallah: Sahyoniyawa Za Su Kwashi Kashinsu A Hannu Matukar Suka Kaddamar Da Yaki Kan Hizbullah
Oct 01, 2017 10:23Shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon Sayyid Hasan Nasrallah ya ja kunnen haramtacciyar kasar Isra'ila da cewa za su debi kashinsu a hannun matukar gigi ya debe su suka kaddamar da yaki a kan kungiyar Hizbullah yana mai kiran yahudawan da suka yiyo hijira zuwa "Isra'ila" da su gaggauta komawa inda suka fito.