-
Sojojin Lebanon Sun Dakatar Da Bude Wuta Don Sasantawa Kan Sojojin Da Ke Hannun Daesh
Aug 27, 2017 11:49Sojojin kasar Lebanon sun dakatar da bude wuta da mayakan kungiyar Daesh a Lebanon don tattauna batun sakin sojojin kasar da ke hannun Daesh.
-
Sojojin Iraki Sun Kwato Sama Da 90% Na Garin Tal Afar Daga Hannun Da'esh
Aug 27, 2017 04:56Kakakin rundunar hadin gwiwa ta kasar Iraki Birgediya Janar Yahya Rasool ya bayyana cewar dakarun kasar da suke samun daukin dakarun sa kai na Hashd al-Sha'abi sun sami nasarar kwato sama da kashi 90% na birnin Tal Afar daga hannun 'yan ta'addan Da'esh, kuma nan gaba kadan za su kwace dukkanin birnin.
-
Libya: An Kama Bayahude Da Ya yi Badda Bami Yana Limanci
Aug 26, 2017 19:01Jami'an kasar Libya sun sanar da cewa mutumin da suka kama a matsayin kwamandan kungiyar Da'esh, yana aiki ne da kungiyar leken asirin Haramtacciyar Kasar Isra'ila ne ta Mosad.
-
An Gano Makeken Kabari Da Aka Bisne Mutane 500 A Birni Mausil
Aug 26, 2017 16:15Dakarun kasar Iraki sun gano wani makeken kabarin na bai daya a kusa da gidan yarin kungiyar ta'addancin ISIS a birnin Mausil babban birnin jihar Nainuwa dake arewacin kasar
-
Gwamnatin Kasar Turkiyya Ta Mika Yan Ta'adda Ukku Ga Kasar Tunisia
Aug 26, 2017 12:47Kakakin kotunan na musamman don hukunta yan ta'adda a kasar Tuniya ya bada sanarwan cewa kotunan sun karbi yan ta'adda guda ukku daga kasar Turkiya kuma sun jefa su a cikin kurkuku a kasar.
-
Yan Kungiyar Ta'addanci Ta Da'ish Sun Fille Kawunan Mutane 11 A Kasar Libiya
Aug 23, 2017 19:02Wasu gungun 'yan bindiga sun kai hari kan wani wajen binciken ababan hawa a yankin kudancin birnin Tripoli fadar mulkin kasar Libiya, inda suka fille kawunan mutane 11 kuma 9 daga cikinsu sojojin gwamnatin kasar.
-
Hadi Amiri: Mafi Yawan 'Yan Ta'addan ISIS A Tal Afar 'Yan Kasashen Waje Ne
Aug 21, 2017 19:14Daya daga cikin manyan kwamandojin dakarun sa kai na kasar Iraki Hadi Al-amiri ya bayyana cewa, mafi yawan mayakan 'yan ta'addan Daesh da ke cikin garin tal Afar 'yan kasashen ketare ne.
-
Sojojin Labanon Sun Kaddamar Da Hare-Haren Korar 'Yan Kungiyar Da'esh Daga Kasar
Aug 19, 2017 16:35Babban hafsan sojojin kasar Labanon Sojojin Janar Joseph Aoun ya bayyana cewar sojojin kasar sun kaddamar da hare-haren zuwa sansanonin 'yan kungiyar ta'addancin nan ta Da'esh da suke gabashin kasar da nufin fatattakansu daga yankunan kasar da suke rike da su.
-
Hizbullah: Manufar ISIS Ita Ce Bakanta Fuskar Musulunci A Idon Duniya
Aug 19, 2017 05:40Kungiyar Hizbullah a kasar Lebanon ta yi tir da Allah wadai da harin ta’addancin da aka kai birnin Barcelona na kasar Spain, tare da bayyana hakan a matsayin hankoron bata sunan addinin muslunci.
-
Palasdinu: Da'esh Ta Dauki Alhakin Kashe Kwamandan Kungiyar Hamas
Aug 18, 2017 06:40A jiya alhamis ne dai aka kai harin kunar bakin wake a yanki9n Rafaha da ke kan iyakar palasdinu da Gaza, wanda ya yi sanadin shahadar NIdhal al-ja'afari, da yake daya daga kwamandojin Izzuddin alkassam.