-
Qatar Ta Gode Wa Iran Saboda Kokarinta Na Magance Rikicin Da Ya Kunno Kai Tsakaninta Da Saudiyya
Jun 10, 2017 17:11Ministan harkokin wajen kasar Qatar Muhammad bn Abdurrahman Al Thani ya jinjinawa Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kuma gode mata saboda irin kokarin da take yi wajen magance rikicin da ya kunno kai tsakaninta da wasu kasashen larabawa karkashin jagorancin kasar Saudiyya.
-
Iran : An Cafke Mutane 48 Bisa Zargin Alaka Da Harin Tehran
Jun 10, 2017 05:52A ci gaba da binciken da ake biyo bayan harin Tehran wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 17, ma'aikatar tattara bayannan sirri ta Iran ta ce an cafke mutane 48 da ake zargi da hannu a jerin hare-haren na ranar Laraba data gabata.
-
Iran : Maharan Tehran Sun Samu Horon Ta'addanci A Mosul Da Raqqa
Jun 08, 2017 18:14Ma'aikatar tattara bayanan sirri ta Iran ta bayyana sunayen maharan da suka kai jerin hare hare ta'addanci a birnin Tehran a Jiya Laraba.
-
Rundunar 'Yan Sandan Tehran: An Kama Mutane 5 Da Ake Zargi Da Harin Hubbaren Imam Khumaini
Jun 08, 2017 05:23Shugaban 'yan sandan birnin Tehran, babban birnin Jamhuriyar Musulunci ta Iran ya bayyana cewar jami'an tsaron kasar sun kama mutane biyar da ake zargi da hannun cikin harin ta'addancin da aka kai haramin Imam Khumaini (r.a) a jiya yana mai jaddada cewa a halin yanzu dai birnin na Tehran yana cikin aminci babu wata damuwa.
-
Jagora: Juyin Juya Halin Musulunci Ya Samar Wa Al'ummar Iran Mutumci Da Kuma 'Yancin Kai
Jun 04, 2017 18:03Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bayyana cewar juyin juya halin Musulunci da marigayi Imam Khumaini (r.a) ya jagoranta a Iran ya samar wa mutanen Iran mutumci da kuma 'yancin kai, yana mai sake jaddada aniyar al'ummar Iran na ci gaba da riko da tafarkin marigayi Imam.
-
Ana Gudanar Da Tarurrukan Juyayin Rasuwar Imam Khumaini (r.a) A Duk Fadin Iran
Jun 04, 2017 05:35A yau ne ake gudanar da bukukuwan juyayin rasuwar marigayi Imam Khumaini (r.a) wanda ya assasa Jamhuriyar Musulunci ta Iran a duk fadin kasar ta Iran inda ake sa ran a yammacin yau Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei zai gabatar da jawabi kan hakan a hubbaren marigayi Imam din da ke wajen birnin Tehran.
-
Iran Za Ta Dauki Nauyin Wani Shiri Na Kur'ani A Afirka Ta Kudu
Jun 03, 2017 19:26Ofishin kula da harkokin yada al'adun muslunci na kasar Iran a Afirka ta kudu ya dauki nauyin shirya wa dalibai musulmi tarukan bayar da horo a kan kur'ani a cikin watan Ramadan.
-
Iran Na Mutunta Yarjejeniyar Nukiliya - AIEA
Jun 02, 2017 15:38Hukumar kula da makamashi ta kasa da kasa (AIEA) ta ce Iran na ci gaba da mutunta yarjejeniyar nukiliyar data cimma da mayan kasashen duniya.
-
Shugaban Iran Ya Meka Sakon Ta'aziyarsa Ga Takwaransa Na Afganistan
Jun 02, 2017 06:28Shugaban Kasar Iran Dakta Hasan Rauhani ya meka sakon ta'aziyar sa ga Takwaransa na kasar Afganistan da kuma iyalan wandanda harin ta'addancin da aka kai birnin Kabul ya ritsa da su.
-
Bunkasar Alaka Tsakanin Kasashen Iran Da Kenya Yana Ci Gaba Da Habaka A Dukkanin Bangarori
Jun 01, 2017 19:21Jakadan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a kasar Kenya ya bayyana cewa: Alaka tsakanin kasashen Iran da Kenya tana ci gaba da habaka musamman a fuskar tattalin arziki a cikin 'yan shekarun nan.