-
Jami'an 'Yan Sandan Gwamnatin Saudiyya Sun harbe Wani Farar Hula A yankin Awamiyyah
Jun 23, 2016 02:23Jami'an 'yan sanda na kasar Saudiyya sun harbe wani farar hula har lahira a garin Al-awamiyyah da ke gabacin kasar ba tare da bayyana wani dalili na yin hakan ba.
-
'Yan Siyasar Masar Sun Yi Maraba Da Hukunci Soke Yarjejeniyar Mika Tsibirai Ga Saudiyya
Jun 22, 2016 11:44Rahotanni daga kasar Masar sun bayyana cewar da dama daga cikin kungiyoyi, jam'iyyu da 'yan siyasar kasar sun yi maraba da hukuncin da wata kotun kasar ta yanke na soke yarjejeniyar da gwamnatin kasar ta cimma da Saudiyya na mika mata ikon wasu tsibirai guda biyu na kasar.
-
Ministan Harkokin Wajen Iraki Ya Soki Saudiyya Da Tsoma Baki Cikin Harkokin Cikin Gidan Kasar
Jun 19, 2016 06:34Ministan harkokin wajen kasar Iraki Dakta Ibrahim Ja'afari yayi kakkausar suka ga kalaman jakadar kasar Saudiyya a kasar Thamer al-Sabhan yana mai cewa hakan tsoma baki ne cikin harkokin cikin gidan kasar Irakin da ba za a taba amincewa da shi ba.
-
Dakarun Kasar Yemen Na Ci Gaba Da Samun Nasarori A Kan Sojojin Kasar Saudiyya
Jun 14, 2016 01:00Rahotanni daga kasar Yemen sun bayyana cewar sojoji da dakarun sa kai na kasar Yemen na ci gaba da mayar da martani ga ci gaba da hare-haren wuce gona da irin sojojin Saudiyyan da kawayenta a kan al'ummar kasar.
-
Ayat. Kermani: Saudiyya Ta Fada Tarkon Amurka Da Yahudawan Sahyoniya
Jun 10, 2016 13:43Na'ibin limamin Juma'ar birnin Tehran Ayatullah Muhammad Ali Muwahhidi Kermani yayi kakkausar suka ga siyasar nuna kiyayyar ga al'ummomin yankin Gabas ta tsakiya da Saudiyya ta ke gudanarwa yana mai cewa Saudiyyan ta fada tarkon Amurka da haramtacciyar kasar Isra'ila.
-
Martani Akan Cire Saudiyya Daga Cikin Kasashe Masu Cin Zarafin Kananan Yara.
Jun 09, 2016 02:14An bukaci sake Mayar Da Saudiyya cikin Jerin kasashen da ke cin zarafin kananan yara.
-
Kungiyoyin Kare Hakkokin Bil'adama Sun Soki Matsayar MDD Na Cire Saudiyya Daga Jerin Masu Take Hakkokin Yara
Jun 08, 2016 01:08Kungiyoyin kare hakkokin bil'adama na kasa da kasa sun yi kakkausar suka ga matsayar Majalisar Dinkin Duniya (MDD) na cire sunan Saudiyya daga jerin kasashen da suke take hakkokin kananan yara.
-
An Kama Wani Dan Sandan Saudiyya A Masar Bisa Zargin Fyade Wa Wata Karamar Yarinya
Jun 02, 2016 12:47Rahotanni daga kasar Masar sun bayyana cewar jami'an tsaron kasar sun kama wani dan sandan kasar Saudiyya bisa zargin da ake masa na yin fyade wa wata yarinya 'yar shekaru 10 a duniya a wani yanki na shakatawa a kasar.
-
Kotun Masarautar Iyalan Gidan Saud Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Masu Fafutuka 14
Jun 01, 2016 06:09Kotun masarautar mulkin mulukiya ta iyalan gidan Saud ta yanke hukuncin kisa kan wasu mutane 14 dukkaninsu masu fafutuka, saboda dalilai na siyasa.
-
Ruhani: Isra'ila Ce Za Ta Amfana Da Kafar Ungulun Da Saudiyya Take Wa Aikin Hajji
May 31, 2016 00:55Shugaban kasar Iran Dakta Hasan Ruhani ya bayyana cewar kafar ungulun da kasar Saudiyya ta yi da ya kai ga hana mutanen Iran zuwa aikin hajjin bana wani lamari ne da zai amfani haramtacciyar kasar Isra'ila da manufofinta a yankin Gabas ta tsakiya.