-
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Fatattakin 'Yan Boko Haram Da Kashe 10 Daga Cikinsu
Jan 14, 2017 14:43Rundunar Sojan kasa ta Nijeriya ta sanar da cewa dakarunta sun sami nasarar dakile wani harin da 'yan kungiyar Boko Haram suka kawo wa wani sansanin sojojin a jihar Borno inda suka kashe alal akalla 'yan ta'addan guda 10 da kuma raunata wasu da dama.
-
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Sanar Da Gano Gawawwakin Sojojinta 16 Da Suka Bace
Jan 12, 2017 02:00Rundunar Sojin Nijeriya ta sanar da gano gawarwakin sojojinta 16 daga cikin 46 da aka sanar da bacewarsu sama da makonni shida da suka gabata a bakin rafin Yobe da ke arewa maso gabashin kasar.
-
Najeriya: An Kashe 'Yan ta'addar Boko Haram 15 A Jahar Yobe
Jan 09, 2017 02:56Wasu 'yan kungiyar Boko Haram 15 Sun halaka bayan da sojoji su ka kashe su a wani yunkurin kai hari a jahar Yobe.
-
Sojojin Nijeriya Sun Kama 'Yan Boko Haram 1400 Cikin Kwanaki 8 Da Suka Gabata
Jan 06, 2017 14:19Rundunar sojin Nijeriya ta sanar da cewa cikin kwanaki takwas din da suka gabata, sojojin Nijeriyan sun sami nasarar kame kimanin mutane 1,400 da ake zargi 'yan kungiyar ta'addancin nan ta Boko Haram ne.
-
An Kashe Yan Mata Ukku Yan Kunan Bakin Wake A Kusa Da Garin Madagali Na Jihar Adamawa
Jan 05, 2017 13:16Majiyar jami'an tsaro a Nigeria sun bayyana cewa jami'an tsaro a wani kauye kusa da garin Madagali na jihar Adamawa a tarayyar Nigeria sun kashe yan mata ukku wadanda suka yi damara da boma bomai don tarwatsa kansu a cikin mutane a garin kafin su aiwatar da shirin nasu
-
Sojojin Sun Kama Wani Jami'in Gwamnatin Borno Saboda Boye Dan Boko Haram
Jan 02, 2017 14:25Gwamnatin jihar Borno ta tabbatar da labarin da ke cewa sojoji sun yi awun gaba da wani shugaban karama a jihar Shettima Mafa saboda laifin ba wa wani dan kungiyar Boko Haram mafaka a gidansa da ke Maiduguri babban birnin jihar Borno.
-
Jami'an Hukumar SSS Sun Kama 'Yan Ta'addan Boko Haram A Kano
Dec 31, 2016 02:19Hukumar jami'an tsaron farin kaya ta Nijeriya (SSS) ta sanar da samun nasarar kame wasu mutane uku da ake zargin cewa mayakan kungiyar ta'addancin nan ta Boko Haram ne a kauyen Dirbunde da ke karamar hukumar Takai da ke jihar Kano ta Nijeriyan.
-
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Yi Watsi Da Sabon Bidiyon Shekau, Farfaganda Ce Kawai
Dec 30, 2016 06:56Rundunar Sojin Nijeriya ta yi watsi da ikirarin shugaban kungiyar Boko Haram Abubakar Shekau yayi cikin wani sabon faifan bidiyon da ya fitar inda ya ce suna nan a Dajin Sambisa, inda ta ce in da gaske ne ya fadi inda yake a cikin dajin mana.
-
Najeriya: An dakile yunkurin kai harin ta'addanci A Birnin Ikko Da Ke Yammacin Kasar.
Dec 29, 2016 14:17"Yan sandan Najeriya Sun dakile wani yunkurin kai hari da bama-bamai a birnin Lagos.
-
Sojin Nijeriya: Za'a Mai Da Dajin Sambisa Wajen Horon Sojoji
Dec 27, 2016 07:47Babban hafsan hafsoshin sojin kasa na Najeriya Laftanar Janar Tukur Yusuf Buratai ya sanar da cewa za a mayar da Dajin Sambisa da ke jihar Borno a matsayin sansanin bayar da horo ga sojojin kasar bayan da sojojin suka sami nasarar kwace dajin daga hannun 'yan kungiyar Boko Haram a kwanakin baya.