-
Sheikh Nabil Kawuk: "Yan Sahayoniya Sun Fi Tsoron Yaran Palasdinuwa Akan Sarakunan Larabawa
Dec 16, 2017 15:39Sheikh Kawuk wanda dan majalisar kungiyar Hizbullah ne ya ce; Boren da yaran palasdinawa suke yi ya fi tsorata 'Yan sahayoniya akan sarakunan larabawa.
-
Kungiyar Ma'aikatan Tunusiya Ta Soki Kungiyar Kasashen Larabawa
Nov 22, 2017 07:54Babban saktaren kungiyar ma'aikatan tunusiya ta soki kungiyar kasashen larabawa a game da matakin da ta dauka a kan kungiyar hizbullah ta kasar Lebanon.
-
Wani Dan Gwagwarmaya A Kasar Aljeriya Ya Zargi Mahukuntan Saudiyya Da Hada Kai Da H.K.Isra'ila
Nov 14, 2017 02:48Daya daga cikin 'yan gwagwarmayar Aljeriya da suka yi yakin 'yantar da kasar daga mulkin mallakar kasar Faransa, kuma mamba a kungiyar National Liberation Front ta kasar ya bayyana cewa: Mahukuntan Saudiyya sun hada kai ne da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila da nufin wanzar da bakar siyasarsu a yankin gabas ta tsakiya.
-
Abdul-Fatah Al-Sisi: Masar Ba Zata Shiga Wani Rikici Da Kungiyar Hizbullahi Ta Kasar Labanon Ba
Nov 08, 2017 02:43Shugaban kasar Masar ya bayyana cewar gwamnatinsa ba zata shiga cikin wani rikici da kungiyar Hizbullahi ta kasar Labanon ba.
-
Sayyid Nasrallah: Amurka Ce Take Hana Yakar Da'esh/Saudiyya Ce Tushen Fitina A Yankin G/Tsakiya
Oct 08, 2017 13:34Shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon Sayyid Hasan Nasrallah ya bayyana cewar Amurka ce take hana kokarin da ake yi na ganin karshen kungiyar ta'addancin nan ta Daesh, kamar yadda kuma Saudiyya da H.K.Isra'ila su ne ummul aba'isin din rashin tsaron da ake fuskanta a yankin Gabas ta tsakiya.
-
Sayyid Nasrallah: Sahyoniyawa Za Su Kwashi Kashinsu A Hannu Matukar Suka Kaddamar Da Yaki Kan Hizbullah
Oct 01, 2017 06:53Shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon Sayyid Hasan Nasrallah ya ja kunnen haramtacciyar kasar Isra'ila da cewa za su debi kashinsu a hannun matukar gigi ya debe su suka kaddamar da yaki a kan kungiyar Hizbullah yana mai kiran yahudawan da suka yiyo hijira zuwa "Isra'ila" da su gaggauta komawa inda suka fito.
-
Sayyid Nasrallah: Za Mu Gutsure Hannun Duk Wanda Ya So Wuce Gona Da Iri Kan Labanon
Aug 31, 2017 13:26Shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon Sayyid Hasan Nasrallah ya ja kunnen masu son wuce gona da iri kan kasar Labanon da cewa za su debi kashinsu a hannu don kuwa lokacin wuce gona da irin ya wuce.
-
Sayyid Nasrallah: 'Yan Da'esh Ba Su Da Wata Mafita Face Mika Kai
Aug 29, 2017 01:10Shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon, Sayyid Hasan Nasrallah ya bayyana cewar 'yan kungiyar ta'addancin nan ta Da'esh da aka fatattaka daga kan iyakokin Siriya da Labanon ba su da wata mafita face kawai su mika kansu ga dakarun gwagwarmaya.
-
Sayyid Nasrallah: Isra'ila Tana Tsoron Sake Kai Hari Labanon Saboda Karfin Hizbullah
Aug 13, 2017 12:32Shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon Sayyid Hasan Nasrallah ya bayyana cewar zamanin barazanar 'Isra'ila' ya wuce kuma ba zai dawo ba har abada, don kuwa ta san cewa karfin kungiyar Hizbullah ya karu sama da na lokacin yakin shekara ta 2006.
-
Dakarun Hizbullah 5 Da Jabhatun Nusra Ta Sace Sun Dawo Gida
Aug 04, 2017 06:08Rahotanni daga kasar Labanon sun bayyana cewa ana ci gab da gudanar da bukukuwan farin ciki don maraba da dakarun kungiyar Hizbullah na kasar su 5 da suka dawo gida bayan sama da shekara guda a hannun 'yan kungiyar ta'addancin nan ta Jabhatun Nusra' da ke da alaka da kungiyar Al-Qa'ida.