-
Wasu Bama-Bamai Sun Fashe A Filin Jirgin saman Birnin Brussels, Na Kasar Belgium.
Mar 22, 2016 10:54Rahotanni daga kasar Belgium sun bayyana cewar wasu bama bamai guda biyu sun fashe a filin jirgin sama na Zaventem da tashar jirgin kasa na Malbeek da ke birnin Brussels, babban birnin kasar Belgium din, inda wasu rahotanni suka ce alal akalla mutane 13 sun mutu wasu da dama kuma sun sami raunuka.
-
Hukumomi Sun Ce An Kashe Daya Daga Cikin Maharan Kan Sojojin Turai A Mali
Mar 22, 2016 10:16Rahotanni daga kasar Mali sun jiyo mahukuntan kasar suna fadin cewa jami'an tsaron kasar sun sami nasarar hallaka daya daga cikin 'yan bindigan da suka kai hari wani otel a Bamako babban birnin kasar inda sojojin kungiyar Tarayyar Turai ke amfani da shi don bai wa jami'an tsaron Mali horo.
-
An Kama Mutane Biyu A Guinea Da Ake Zargi Da Hannu Cikin Harin Ivory Coast
Mar 20, 2016 09:44Rahotanni daga kasar Guinea Conakry sun bayyana cewar jami'ar tsaron kasar sun sami nasarar cafke wasu mutane biyu da ake zargi da hannu cikin harin ta'addancin da aka kai kasar Ivory Coast a kwanakin baya.
-
Jami'an Tsaron Somaliya Sun Hallaka 'Yan Ta'addan Al-Shabab Guda 60
Mar 18, 2016 17:49Jami'an tsaro a yankin Puntland mai kwarya kwaryar cin gashin kai a kasar Somaliya sun sanar da samun nasarar hallaka wasu 'yan kungiyar ta'addancin nan ta Al-Shabab su 60 a wani harin da suka kai musu da ya ba su damar kwace wasu yankuna da 'yan ta'addan suke rike da su.
-
Lavrov: Ficewar Sojojin Rasha Daga Siriya, Don Karfafa Tattaunawar Sulhu Ne
Mar 16, 2016 17:21Ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergei Lavrov ya bayyana cewar kasar Rasha ta janye wani bangare na sojojinta daga kasar Siriya ne don karfafa shirin tattaunawar sulhu da ake yi da nufin kawo karshen rikicin kasar cikin ruwan sanyi.
-
Tarayyar Afirka Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta'addancin Ivory Coast
Mar 14, 2016 17:25Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) ta yi Allah wadai da harin ta'addancin da aka kai wani Otel a kasar Ivory Coast a jiya kamar yadda ta sanar da ta'aziyya da kuma aihininta ga gwamnati da kuma al'ummar kasar da sauran wadanda abin ya shafa.
-
Hukumomin Turkiyya Sun Ce Wata Mace 'Yar PKK Ce Ta Kai Harin Birnin Ankara
Mar 14, 2016 16:19Hukumomi a kasar Turkiyya sun bayyana cewar sun gano mace guda daga cikin mutane biyun da ake zargi da kai mummunan harin kunar bakin wake da aka kai birnin Ankara a jiya Lahadi da yayi sanadiyyar mutuwa da raunata wani adadi mai yawa na mutanen kasar.
-
Amurka Ta Sanar Da Hallaka 'Yan Ta'addan Al-Shabab 150 A Somaliya
Mar 08, 2016 05:44Rundunar sojin Amurka ta sanar da cewa ta samu nasarar hallaka sama da mayakan kungiyar 'yan ta'addan nan ta Al Shabab ta kasar Somaliya 150 a wani hari da suka kai musu da jirgin yaki mara matuki.
-
Cikin Wasiyyarsa, Bin Laden Ya Bar Dala Miliyan 29 Don Ayyukan Al-Qa'ida
Mar 02, 2016 05:27Wasiyyar tsohon shugaban kungiyar ta'addancin nan ta Al-Qa'ida Usama Bin Laden da aka fitar, na nuni da cewa ya bar dala miliyan 29 don ci gaba da gudanar da abin da ya kira jihadi da kungiyar tasa take yi.
-
Sojojin Kasar Masar Sun Sanar Da Hallaka Wasu 'Yan Ta'adda 40 A Kasar
Feb 12, 2016 04:42Rahotanni daga kasar Masar sun bayyana cewar sojojin kasar sun sami nasarar hallaka wasu 'yan ta'adda su 40 bugu da kari kan raunata wasu da dama a wani harin kwanton bauta da suka kai musu.