-
Azhar Ta Taya Kiristocin Masar Alhini Kan Harin Ta'addancin Da Daesh Ta Kai Kansu
Nov 03, 2018 19:12Babban malamin cibiyar Azhar Sheikh Ahmad Tayyib ya aike da sakon taya alhini ga jagoran kiristocin kasar Masar, dangane da harin ta'addancin da mayakan kungiyar Daesh suka kai kansu.
-
Jami'ar Azhar Ta Yi Allah Wadai Da Halin Ko In Kulan Da Ake Nuna Wa Danyen Aikin 'Isra'ila'
Apr 07, 2018 11:18Jami'ar al-Azhar ta kasar Masar ta yi kakkausar suka dangane da irin shiru da halin ko in kula da manyan kasashen duniya da cibiyoyin kasa da kasa suke nunawa irin wuce gona da iri na baya-bayan nan da haramtacciyar kasar Isra'ila take yi wa al'ummar Palastinu.
-
An Bude Taron Kasa Da Kasa Na Nuna Goyon Baya Ga Kudus A Kasar Masar
Jan 17, 2018 18:20A yau Laraba ce shugaban Jami'ar Al-Azhar ta kasar Masar Sheikh Ahmad Al-Tayyib ya bude wani taron kasa da kasa na nuna goyon baya ga birnin Kudus da Masallacin Al-Aqsa a birnin Alkahira, babban birnin kasar ta Masar don tattauna hanyoyin da za a bi wajen ba da kariya ga birnin na Kudus daga barazanar da yake fuskanta.
-
Al-Azhar Ta Yi Suka Kan Zancen Trump Na Wulakanta Wasu Kasashe
Jan 14, 2018 18:59Jami'ar Al-Azhar ta kasar Masar ya yi Allah wadai da kalaman wulakanci da kaskanta wasu kasashen duniya wanda shugaban Amurka ya yi
-
Damuwar Jami'ar Azhar A Game Da halin Da Musulmi Ke Cikin A Myammar
Jan 04, 2018 19:04Cikin wata sanarwa da ta fitar jami'ar Azhar ta kasar Masar ta bayyana damuwarsa kan halin da al'ummar musulmin Rohinga ke ciki a kasar Myammar
-
Jami'ar Azhar Ta Kasar Masar Ta Bukaci Shirya Taron Kasa Da Kasa Kan Birnin Qudus
Dec 10, 2017 19:08Jami'ar Azhar ta kasar Masar ta yi gargadi kan irin mummunan hatsarin da ke tattare da matakin da shugaban kasar Amurka ya dauka na shelanta birnin Qudus a matsayin fadar mulkin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila, don haka ta bukaci shirya zaman taron kasa da kasa kan batun na Qudus.
-
Jami'ar Al-Azhar Ta Yi Allah Wadai Da Kisan Kiyashin Da Ake Yi Wa Musulman Myammar
Sep 06, 2017 11:09Jami'ar Al-Azhar ta kasar Masar ta nuna tsananin damuwarta dangane da kisan kiyashin da sojoji da mabiya addinin Buddha na kasar Myammar suke yi wa musulmin Rohingya na kasar tana mai bayyana hakan a matsayin wani abin kunya ga cibiyoyi da kasashen duniya.
-
An Yi Allawadai Da Keta Alfarmar Wani Masallaci A Faransa
Jul 26, 2017 12:03Bangaren da ke sa ido kan kyamar musulmi a cikin kasashen nahiyar turai da ke karkashin kulawar cibiyar Azhar ya yi Allawadai da kan keta alfarmar wani masallaci na musulmi a gabashin kasar Faransa.
-
Al-Azhar Ta Ja Kunnen "Isra'ila" Kan Ci Gaba Da Keta Hurumin Masallacin Kudus
Jul 22, 2017 05:48Jami'ar Al-Azhar ta kasar Masar ta ja kunnen haramtacciyar kasar Isra'ila dangane da ci gaba da keta hurumin masallacin Kudus mai alfarma da take yi, don kuwa hakan lamari ne da musulmi ba za su iya rufe ido kansa ba.
-
Cibiyar Azhar Ta Yi Allawadai Da Kai Hari A Kan Masallata A London
Jun 21, 2017 05:50Babbar cibiyar addini ta Azahar da ke kasar Masar ta yi tir da Allah wadai da harin da aka kai kan musulmi bayan kammala salla a birnin London.