-
Janar Suleimani: An Kirkiro Da’esh Ne Don Raunana Kasar Iran
Oct 06, 2016 10:58Kwamandan dakarun Qudus na dakarun kare juyin juya halin Musulunci na kasar Iran Manjo Janar Qassem Suleimani ya bayyana cewar and kirkiro kungiyar Da’esh da sauran kungiyoyin ‘yan ta’adda masu kafirta mutane ne da nufin raunana kasar Iran.
-
Shugaban Mali Ya Ja Kunnen MDD Dangane Da Karfin Da 'Yan Ta'adda Suke Yi A Kasar
Sep 23, 2016 17:41Shugaban kasar Mali Ibrahim Boubacar Keita ya ja kunnen Majalisar Dinkin Duniya da cewa rashin aiwatar da yarjejeniyar sulhun da aka cimma a kasar yana taimakon 'yan kungiyoyin ta'addancin nan ta Al-Qa'id da sauran kungiyoyin da suke da alaka da kungiyar ISIS ci gaba da samun tasiri da gindin zama a kasar.
-
Gwamnatin Iraki Ta Sanar Da Fara Hare-Haren Kwato Musil Daga Hannun Da'esh
Sep 20, 2016 09:22Gwamnatin kasar Iraki ta sanar da cewa sojojin kasar tare da daukin dakarun sa kai sun fara hare-haren kwato garin Mosul daga hannun 'yan ta'addan Da'esh da suke rike da shi da kuma mayar da shi babbar tungarsu.
-
Jiragen Yakin Siriya Da Rasha Sun Kai Hari Kan Sansanonin 'Yan Da'esh A Dayr al-Zawr
Sep 19, 2016 11:25Jiragen yakin Siriya Da Rasha sun kai wasu hare-hare kan wasu wajajen da 'yan ta'addan kungiyar Da'esh suke a garin Dayr al-Zawr bayan wasu hare-haren da Amurka ta kai kan sojojin Siriyan a kusa da wajen da yayi sanadiyyar mutuwar sojojin Siriyan su 62, lamarin da ya share wa 'yan kungiyar Da'esh din fagen kai hari kan sojojin Siriyan.
-
Firayi Ministan Libiya Ya Jaddada Aniyar Gwamnatinsa Ta Ci Gaba Da Yakar Kungiyar ISIS
Sep 01, 2016 17:20Firayi ministan gwamnatin hadin kan kasa ta kasar Libiya Fa'iz al-Siraj ya bayyana aniyar gwamnatinsu ta ci gaba da yakar kungiyar ta'addancin nan ta Da'esh (ISIS) har sai sun fatattake su daga kasar.
-
Kungiyar ISIS Ta Ce Ita Ke Da Alhakin Kaddamar Da Harin Birnin Nice Na Faransa
Jul 16, 2016 12:11Kungiyar 'yan ta'adda ta ISIS ta sanar da cewa ita ce ke da alhakin kaddamar da harin birnin Nice na kasar Faransa, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 84 tare da jikkatar wasu fiye da 200.
-
Kasar Libiya Ta Kaddamar Da Sabon Shirin Fada Da Ta'addanci A Kasar
Jun 19, 2016 11:03Rahotanni daga kasar Libiya sun bayyana cewar shugaban majalisar kasar Aqilah Saleh ya kirayi al'ummar kasar da su hada kai wajen yakar kungiyoyin 'yan ta'adda a kasar
-
Al'ummar Iraki Na Ci Gaba Da Bukukuwan Kwato Fallujah Daga Hannun Da'esh
Jun 18, 2016 11:00Dubun dubatan al'ummar kasar Iraki ne suka fito kan titunan garuruwa daban-daban na kasar don nuna farin cikinsu da kwace garin Fallujah mai matukar muhimmanci da sojojin kasar da suke samun dauki dakarun sa kai suka yi a jiya daga hannun 'yan kungiyar ta'addancin nan ta Da'esh wadanda suke rike da garin sama da shekaru biyu.
-
Wani Dan Ta'addan ISIS Ya Hallaka Wani Jami'in 'Yan Sandan Faransa Da Matarsa A Paris
Jun 14, 2016 05:32Rahotanni daga kasar Faransa sun bayyana cewar wani mutum da aka ce yana da alaka da kungiyar ta'addancin nan ta Da'esh (ISIS) ya hallaka wani babban jami'in 'yan sandan Faransan da matarsa a gidansu da ke kusa da birnin Paris, babban birnin kasar Faransan kafin 'yan sanda su hallaka shi, shi ma.
-
Sojojin Iraki Sun Hallaka Mataimakin Bagdadi Da Wasu Manyan Kwamandojin Da'esh A Iraki
May 31, 2016 05:22Rundunar sojin kasar Iraki ta sanar da samun nasarar hallaka daya daga cikin manyan mataimakan shugaban kungiyar ta'addancin nan ta Da'esh (ISIS) Abubakar Al-Bagdadi da wasu manyan kwamandojin kungiyar a kasar Irakin.