-
ECOWAS Za Ta Ci Gaba Da Kokarin Magance Rikicin Gambiya Cikin Ruwan Sanyi
Jan 08, 2017 05:52Shugabar kasar Liberiya kana kuma shugabar kungiyar ECOWAS ta tattakin arzikin kasashen yammacin Afirka, Ellen Johnson Sirleaf ta sanar da cewar shugabannin kungiyar za su ci gaba da aikin da suke yi na shiga tsakani da nufin kawo karshen rikicin siyasar da ya kunno kai a kasar Gambiya cikin ruwan sanyi.
-
Gambiya: Babban Hafasan Hafsoshin Sojan Kasar ya Nuna Goya Bayansa Ga Shugaba Jammeh
Jan 05, 2017 07:22Babban Hafsan hafsoshin sojan kasar Gambiya Usman Baji ya nuna cikakken goyon bayansa da na dukkanin sojojin kasar ga Shugaba Yahya Jammeh.
-
Shugaban Hukumar Zaben Gambiya Ya Tsere
Jan 03, 2017 18:18Rahotanni daga Gambiya na cewa shugaban hukumar zabe ta kasar ya tsere daga kasar sakamakon barazanar rasa ransa.
-
Shugaban Kasar Gambia Ya Zargi ECOWAS Da Shelanta Yaki A Kan Kasarsa
Jan 01, 2017 15:51Shugabann kasar Gambia Yahayah Jemeh ya bayyana cewa kungiyar raya tattalin arziki na yammacin Afrika ECOWAS ta shelanta yaki a kan kasarsa.
-
Senegal ta jaddawa wajabcin Warware Rikicin kasar Gambiya Ta Ruwan Sanyi.
Jan 01, 2017 12:04A sakonsa na shiga sabuwar shekara shugaban kasar Senegal ya karfafa aiki da hanya ta sulhu domin kawo karshen takaddamar siyasa a kasar Gambiya.
-
Sojoji Sun Bar Hedikwatar Hukumar Zaben Kasar Gambiya
Dec 30, 2016 10:29Rahotanni daga kasar Gambiya sun bayyana cewar sojojin kasar sun bar hedikwatar hukumar zaben kasar bayan mamaye wajen da suka yi na sama da makonni biyu da kuma korar ma'aikatan da suke wajen.
-
'Yan Adawan Gambiya: Jammeh Zai Zamanto Dan Tawaye Matukar Bai Mika Mulki A 19 Ga Janairu Ba
Dec 29, 2016 11:52Hadin gwiwan jam'iyyun 'yan adawan kasar Gambiya sun bayyana cewar shugaban kasar Yahya Jammeh zai zamanto dan tawaye daga 19 ga watan Janairu matukar dai bai mika mulki a wannan ranar ga zababben shugaban kasar Adama Barrow ba.
-
'Yan Adawar Gambiya: Babu Wata Kotu Da Za Ta Soke Zaben Adamar Barrow Da Aka Yi
Dec 24, 2016 16:48Gamayyar 'yan adawan kasar Gambiya sun yi watsi da sanarwar da kotun kolin kasar ta yi na fara sauraran karar da shugaban kasar Yahya Jammeh ya shigar yana kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasar inda suka ce babu wata kotu a duniyar nan da ta isa ta sauya nasarar da dan takararsu Adamar Barrow ya samu a zaben 1 ga watan Disamban da aka gudanar.
-
ECOWAS Ta Umarci Dakarun Senegal Da Su Zama Cikin Shirin Kifar Da Yahya Jammeh Na Gambia
Dec 23, 2016 18:02Kungiyar bunkasa harkokin tattalin arzikin kasashen yammacin nahiyar Afirka ECOWAS, ta umarci kasar Senegal da ta sanya dakarunta acikin shirin ko ta kwana, domin safke Yahya Jammeh da karfin tuwo, matukar dai yaki mika mulki a karashen wa'adinsa.
-
Kotun Kolin Gambiya Za Ta Saurari Karar Da Shugaba Jammeh Ya Gabatar Mata
Dec 22, 2016 05:51Kotun kolin kasar Gambiya ta sanar da ranar 10 ga watan Janairu mai kamawa a matsayin ranar da za fara sauraran karar da shugaban kasar Yahya Jammeh ya shigar a gabanta inda yake kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasa da aka yi a watan Disamba inda aka sanar da cewa ya sha kaye.