-
Jagora Ya Gana Da Iyalan Shahid Mustafa Badruddeen
May 27, 2016 00:42Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bayyana tsohon babban kwamandan dakarun kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon Shahid Mustafa Badruddeen a matsayin wani jarumi kana kuma tsayayyen dan gwagwarmaya don haka yayi masa fatan samun karin matsayi da daukaka a wajen Allah Madaukakin Sarki.
-
Zarif: Shahadar Kwamandan Hizbullah, Zai Kara Wa Kungiyar Azamar Ci Gaba Da Fada Da Isra'ila Ne
May 13, 2016 12:44Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewar ko shakka babu shahadar babban kwamandan dakarun kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon Shahid Mustafa Badruddeen zai kara wa kungiyar azama da tsayin dakan da take da shi ne wajen fada da haramtacciyar kasar Isra'ila da kuma ta'addanci.
-
Sheikh Na'im Qasim: Shahid Badrudden Ya Dandana Wa Isra'ila Da 'Yan Takfiriyya Kuda
May 13, 2016 12:35Na'ibin shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon Sheik Na'im Qasim ya bayyana cewar babban kwamandan sojin kungiyar Shahid Mustafa Badruddeen wanda yayi shahada yau din nan a kasar Siriya ya dandana wa haramtacciyar kasar Isra'ila da kuma kungiyoyin 'yan takfiriyya masu kafirta musulmi kuda a kasar Siriyan yana mai cewa nan da wani lokaci kadan kungiyar za ta sanar da sakamakon binciken da ta gudanar dangane da harin da aka kai wa babban kwamandan da yayi sanadiyyar shahadarsa.
-
Jagora Yayi Watsi Da Sanya Hizbullah Cikin Kungiyoyin 'Yan Ta'adda Da Saudiyya Da Kawayenta Suka Yi
Apr 20, 2016 06:18Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei yayi Allah wadai da kuma kakkausar suka ga bayyana kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon da wasu kasashen larabawa, bisa matsin lamba da cin hancin da kasar Saudiyya ta ba su, suka yi a matsayin kungiyar ta'addanci yana mai cewa kungiyar Hizbullah dai ta kasance abar alfaharin duniyar musulmi.
-
Jami'an Tsaron Labanon Gano Wata Cibiyar 'Yan Ta'adda Mai Hatsarin Gaske A Kasar
Apr 10, 2016 00:04Rahotanni daga kasar Labanon sun bayyana cewar jami'an tsaron kasar sun sami nasarar ganowa da kuma cafke 'yan wata kungiyar 'yan ta'adda mai hatsarin gaske a kasar.
-
Yan Gudun Hijiran Palasdinawa Da Suke Kasar Lebanon Sun Bukaci Tallafin M.D.D
Apr 06, 2016 13:49Yan gudun hijiran Palasdinawa da suke rayuwa a sansanin 'yan gudun hijira da ke kasar Lebanon sun bukaci tallafin Majalisar Dinkin Duniya domin warware musu wasu daga cikin matsalolinsu.
-
Hizbullah Sun Kai Munanan Hare-Hare Kan Sansanonin ISIS A Gabashin Labanon
Apr 04, 2016 12:40A ci gaba da fatattakan mayakan kungiyar ta'addancin nan ta Da'esh (ISIS) da kuma nesata su daga kasar Labanon, dakarun kungiyar Hizbullah ta kasar sun kai wasu munanan hare-hare a kan sansanonin 'yan kungiyar ta'addancin a yankunan da suke gabashin kasar ta Labanon.
-
Kasar Lebanon Ta Bukaci Samun Hadin Kan Kasashen Duniya A Fagen Yaki Da Ta'addanci
Apr 02, 2016 11:58Ministan harkokin wajen kasar Lebanon ya gabatar da bukatar samun hadin kan dukkanin kasashen duniya a fagen yaki da ta'addanci.
-
Babban Sakataren M.D.Duniya Ya Jaddada Wajabcin Kawo Karshen Rikicin Siriya
Mar 26, 2016 05:15Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya ya jaddada bukatar ganin an kawo karshen duk wani tashe-tashen hankula musamman ayyukan ta'addanci a cikin kasar Siriya.
-
'Yan Majalisar Iran Sun Sake Jaddada Goyon Bayansu Ga Kungiyar Hizbullah
Mar 08, 2016 02:14Sama da 'yan majalisar shawarar Musulunci ta kasar Iran 200 ne suka nuna goyon bayansu ga kungiyar Hizbullah ta kasar Labanon da kuma yin Allah wadai da matsayar da kungiyar larabawan Tekun Fasha na sanya kungiyar cikin kungiyoyin 'yan ta'adda.