-
Masar: An Kashe 'Yan Ta'addar Da Su ka Kai Hari A Yankin Jiza.
Jul 16, 2017 02:20'Yan sandan kasar Masar sun sanar da kashe 'yan ta'adda biyu da su ka kai harin ta'addanci wanda ya kashe jami'an tsaro masu yawa.
-
Wani Mutum Dauke Da Wuka Ya Kashe Mata Biyu 'Yan Yawon Shakatawa A Kasar Masar
Jul 15, 2017 02:01Wani dan ina ga kisa ya kashe wasu mata biyu 'yan yawon shakatawa tare da jikkata wasu hudu na daban a garin Hurghada da ke kusa da gabar teku a shiyar arewa maso gabashin kasar Masar.
-
Malamin Kirista A Masar Ya Ce Addinin Muslunci Ya Barranta Daga ISIS
Jul 14, 2017 06:12Jagoran kiristoci mabiya darikar katolika a kasar Masar ya bayyana addinin muslunci da cewa addini ne da ba shi da alaka da kungiyoyin 'yan ta'adda irin su Daesh da makamantansu.
-
A Kafa Dokar Hana Fita A Wasu Yankuna A Yankin Sina Na Kasar Masar
Jul 11, 2017 02:26Bayan hare haren da aka kaiwa jami'an tsaron Masar a yankin Sani a cikin kwanakin da suka gabata, Priministan kasar ya bada umurnin kafa dokar hana fita a wasu yankuna na Sina.
-
Kotun Sojin Masar Tana Zargin Mutane 292 Da Shirya Makarkashiyar Kashe Shugaban Kasar
Jul 09, 2017 14:31Babban lauyar gwamnatin Masar mai shigar da kara ya maida shari'ar mutane 292 zuwa kotun sojin kasar kan zargin 'yan kungiyar ta'addanci ta Da'ish ne, kuma suna da hannu a shirya makarkashiyar aiwatar da kisan gilla kan shugaban kasar.
-
Masar Za Ta Binciki Mutuwar 'Yan Kasar Ta A Libiya
Jul 09, 2017 06:41Ma'aikatar Harakokin wajen Masar ta sanar da cewa za ta gudanar da bincike a kan mutuwar 'yan kasar ta a kasar Libiya
-
Masar Ta Kori Daliban Indosiya 4
Jul 08, 2017 07:25Masar Ta fitar da daliban jami'ar nan guda 4 'yan kasar Indanosiya da ta zarga da kokarin tayar da hankali
-
Masar: Kungiyar Da'esh Ta Dauki Alhakin Kashe Sojojin Masar Fiye Da 20
Jul 08, 2017 02:20A jiya juma'a ne dai aka kai hari a wuraren biyu na bincike, a yankin Sinaa ta arewa da ya ci rayukan sojoji 23.
-
An Bayyana Wasu Daga Cikin Matakan Da Saudia Da Kawayenta Zasu Dauka A Kan Qatar
Jul 07, 2017 14:33Wani dan majalisar dokokin kasar Masar Ya bayyana wasu matakan da kasashe hudu wadanda suka dorawa kasar Qatar takunkumai zasu dauka bayan rashin gamsuwarsu da amsar da ta bayar kan sharuddansu na farko
-
Kungiyar Human Right Watch Ta Zargi Mahukuntan Masar Da Kame Dalibai 'Yan Kasar China
Jul 07, 2017 02:27Kungiyar kare hakkin bil-Adama ta Human Right Watch ta zargi gwamnatin Masar da kame dalibai 'yan kasar China da suke karatun addinin Islama a cikin kasarta.