-
Sojojin Nijeriya Sun Kashe 'Yan Boko Haram Da Dama A Wani Gumurzu
Nov 20, 2016 08:18Rahotanni daga jihar Borno da ke arewa maso gabashin Nijeriya sun bayyana cewar sojojin Nijeriya sun sami nasarar hallaka wani adadi mai yawa na 'yan kungiyar Boko Haram kana wasu da dama kuma sun sami raunuka a wani gumurzu da ya gudana tsakanin bangarori biyun.
-
Fadar Shugaban Nigeria Ta Musanta Cewa Buhari Ya Ba Wa Clinton Dala Miliyan 500
Nov 19, 2016 07:47Fadar shugaban Nigeria ta musanta cewa shugaban kasar Muhammadu Buhari ya ba wa tsohuwar 'yar takarar shugabancin Amurka da ta sha kaye Hillary Clinton taimakon Dala Miliyan 500 a lokacin da take yakin neman zabe.
-
An Zartar Da Hukuncin Kisa A Kan Wani Dan Nijeriya A Singapore
Nov 18, 2016 09:46Rahotanni daga kasar Singapore sun jiyo mahukuntan kasar suna cewa an zatar da hukuncin kisa a kan wani dan Nijeriya da kuma dan kasar Malaysia saboda samunsu da aka yi da laifin safarar miyagun kwayoyi.
-
'Yan Sandan Sun Tabbatar Da Mutuwar Mutane 6 A Maiduguri
Nov 18, 2016 07:39Rundunar 'yan sandan jihar Borno sun tabbatar da mutuwar mutane 6 sakamakon fashewar wasu tagwayen abubuwa a birnin Maiduguri, babban birnin jihar Bornon Nijeriya.
-
Kotun ICC ta bukaci Gwamnatin Najeriya da ta yi bayyani kan kisan gillar da Sojoji suka yi wa Musulmi a kasar
Nov 17, 2016 14:42Kotun ICC ta bukaci Gwamnatin Najeriya da ta yi mata bayyani kan kisan gillar da Sojoji suka yi wa Musulmi shekarar da ta gabata a kasar
-
Wasu 'Yan Bindiga Dadi Sun Kashe Mutane 6 Da Sace Shanu 700 A Niger
Nov 17, 2016 07:49Rahotanni daga Nijeriya sun bayyaan cewar wasu mutane 6 sun rasa rayukansu kana wasu daruruwan shanu kuma sun bace sakamakon wani harin da barayin shanu suka kai gundumar Kukoki da ke karamar hukumar Shiroro, na jihar Nija da ke arewacin Nijeriyan.
-
Boko Haram Ta Sake Kashe Wani Kwamandan Sojin Najeriya
Nov 15, 2016 14:53Rahotanni dake cin karo da juna a Najeriya na cewa Wa kungiyar Boko Haram ta sake hallaka wani Laftanar Kanal na rundunar sojin kasar.
-
Adadin Mutanan da suka yi shahada sanadiyar harin da 'yan sandar Kano sun kaiwa Masu tattaki ya karu.
Nov 15, 2016 02:24Adadin Mutanan da suka yi shahada sanadiyar buda wuta da 'yan sandar Kano suka yi a kan 'yan uwa musulmi almajiran shekh Ibrahim Elzakzaky ya karu
-
Adadin Mutanan da suka yi shahada sanadiyar harin da 'yan sandar Kano sun kaiwa Masu tattaki ya karu.
Nov 15, 2016 02:21Adadin Mutanan da suka yi shahada sanadiyar buda wuta da 'yan sandar Kano suka yi a kan 'yan uwa musulmi almajiran shekh Ibrahim Elzakzaky ya karu
-
Hukumar NCC Mai Kula Da Kamfanonin Wayoyin Sadarwa A Nigeria Ta Yi Barazanar Ladabtar A Wasu Kamfanonin Wayoyi A Kasar
Nov 14, 2016 13:30Hukumar NCC mai kula da kamfanonin wayoyin sadarwa a Nigeria ta yi barazanar ladabtar da wasu kamfanin Sadarwa wadanda suka hada da manya manyan kamfanoni guda hudu wato MTN, Glo, Etisalat Airtel, da kuma wasu idan sun ci gaba da bude kafar aiko da sakon SMS wanda mutane basa so.