-
Afrika : Mutum 2,600 Harin Ta'addanci Ya Kashe A 2017
Jun 28, 2018 00:51Kimanin hare haren ta'addanci 343 ne aka kiyasta cewa an kai a cikin shekara 2017 da ta gabata a nahiyar Afrika, wadanda suka hadassa mutuwar mutane a kalla 2,600.
-
Kungiyar ECOWAS Na Kokarin Sassanta Rikicin Kasar Togo
Jun 27, 2018 14:34A wannan laraba ce ake sa ran manzannin musamman na kungiyar Cigaban Tattalin Arzikin Yammacin Afirka Ecowas ko Cedeao za su isa birnin Lome na kasar Togo, domin farfado da tattaunawar sulhu tsakanin gwamnati da ‘yan adawar kasar.
-
Moroko Ta Ce: Yan Ta'adda Fiye Da 10,000 Ne Suka Kwararo Cikin Nahiyar Afrika
Jun 27, 2018 08:00Ministan harkokin wajen kasar Moroko ya bayyana cewa: Akwai 'yan ta'adda da suka haura 10,000 da suka shigo cikin kasashen nahiyar Afrika.
-
Shugabannin 'Yan Sanda Na Kasashen ECOWAS Na Taro Kan Yaki Da Ta'addanci
Jun 26, 2018 01:24Shugabannin 'yan sanda da kuma na tsaro na kasashen mambobin kungiyar raya arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS/CEDEAO, sun fara wani taron na yini uku a birnin Abidjan na kasar Ivory Coast mai manufar karfafa hadin guiwa don yaki da ta'addanci.
-
Sudan Ta Kudu : Mashar Da Kiir Zasu Gana A Khartum
Jun 25, 2018 06:06Jagoran 'yan adawa a Sudan ta kudu, Riek Mashar, ya isa a birnin Khartoum na Sudan inda yau Litini zai fara wata tattaunawa da shugaba, Salva Kiir na Sudan ta Kudu, kan batutuwan da bangarorin biyu ke takkadama da juna akansu da suka hada da mulki da kuma tsaro.
-
Russia 2018 : Senegal Ta Yi Kunnen Doki Da Japan 2-2
Jun 24, 2018 12:56A ci gaba da gasar cin kofin kwallon kafa na duniya da Rasha ke karbar bakunci, an tashi kunnen doki tsakanin tawagar kwallon kafa ta Senegal da Japon 2-2 a wasaninsu na biyu biyu da suka buga da maraicen yau a rukunin H.
-
An Kashe Fararen Hula 32 A Tsakiyar Mali
Jun 24, 2018 11:23Rahotanni daga Mali na cewa a kalla fararen hula fulani 32 ne suka rasa rayukansu a wani hari da ake danganta wa dana mafarauta da ake kira ''Dozo'' a yankin.
-
Mutane Da Dama Sun Mutu Bayann Fashewar Wani Abu A Taron Goyon Bayan Firayi Ministan Ethiopia
Jun 23, 2018 06:46Rahotanni daga kasar Ethiopia (Habasha) sun bayyana cewar mutane da dama sun mutu wasu kuma sun sami raunuka sakamakon fashewar wani abu a wajen taron gangamin goyon bayan sabon firayi ministan kasar Abiy Ahmad da dubun dubatan magoya bayansa suka halarta.
-
Najeriya : 'Yan Kunar Bakin Wake Sun Raunana Mutun 15 A Borno
Jun 21, 2018 10:32Rahotanni daga jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya na cewa, mutane akalla 15 sne suka raunana, yayin da wasu 'yan kunar bakin wake biyu mata suka tarwasa kansa a wata barikin soji dake jihar.
-
AU Ta Yaba Da Ci Gaban Da Aka Samu Ta Fuskar Diflomatsiyya Tsakanin Habasha da Eritrea
Jun 21, 2018 09:59Shugaban Kwamitin kungiyar tarayya Afrika, Musa Faki Mahamad, ya yaba da ci gaban da aka samu a baya bayan nan a huldar diflomatsiyya tsakanin kasashen Habasha da Eritrea.