-
Iran Za Ta Kaddamar Da Wasu Tauraron Dan'Adam Guda Uku
Dec 22, 2016 02:19Ministan sadarwa da fasaha na kasar Iran ya sanar da cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran na shirin aikawa da wasu sabbin tauraron dan'adam da masanan kasar suka kera zuwa sararin samaniyya a karshen wannan shekara ta hijira shamsiyya da ke karewa a watan Maris mai kamawa.
-
Shugaban Kasar Iran Ya Isa Kasar Armenia A Cikin Shirin Ziyarar Wasu Kasashe A Yankin
Dec 21, 2016 07:51Shugaban kasar Iran Dr Hassan Ruhani ya isa kasar birnin Yerevan na kasar Armenia a zangonsa na farko na ziyarar wasu kasashen yankin guda ukku.
-
Taron Ministocin Harkokin Wajen Iran, Rasha Da Turkiyya Kan Rikicin Siriya
Dec 20, 2016 14:51Ministan harkokin wajen kasar Iran Dakta Muhammad Jawad Zarif ya bayyana cewar Iran, Rasha da Turkiyya sun fara aiwatar da wani shiri na samo hanya ta diplomasiyya wajen magance rikicin kasar Siriya.
-
Sheikh Kasim: 'Yantar Da Aleppo Ya Rusa Shirin 'Yan Ta'adda
Dec 18, 2016 09:14Mataimakin babban sakataren kungiyar Hizbullah ya bayyana 'yantar da birnin Aleppo daga 'yan ta'adda a matsayin wata babbar nasara, wadda ta kawo karshen mafarkin 'yan ta'adda da masu mara musu baya na kafa wata daular ta'addanci a birnin.
-
Shugabar Hukumar Makamashin Nukiliya Ta Duniya Na Kan Hanyarsa Ta Zuwa Iran.
Dec 17, 2016 02:52Yokiya Amano Zai Zo Iran A Gobe Lahadi
-
Ayatullah Khamenei Yayi Afuwa Wa Wasu Fursunoni Saboda Zagayowar Maulidi
Dec 16, 2016 13:41Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya amince da yin afuwa da kuma rage wa'adin zaman gidan yarin sama da fursunoni 1,200 don murnar zagayowar ranar Maulidin Manzon Allah (s).
-
Ruhani: Iran Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Siriya Har Samun Nasara Ta Gaba Daya
Dec 15, 2016 07:46Shugaban kasar Dakta Hasan Ruhani ya taya takwararsa na kasar Siriya Bashar al-Asad murnar 'yanto garin Halab (Aleppo) daga hannun 'yan ta'addan ISIS yana mai cewa Iran za ta ci gaba da goyon bayan kasar Siriya har sai ta sami nasara a kan fada da ta'addancin da take yi.
-
An Bude Taron Makon Hadin Kai Karo Na 30 A Tehran
Dec 15, 2016 07:42A safiyar yau Alhamis ne aka bude taron kasa da kasa kan hadin kan al'ummar musulmi karo na 30 a nan birnin Tehran, babban birnin Jamhuriyar Musulunci ta Iran, taron da ya sami halartar baki sama da 300 daga ciki da wajen kasar Iran.
-
Wata Kotu A Kasar Kenya Ta Yanke Hukuncin Korar Iraniyawa Biyu Da Take Tuhuma Da Ayyukan Ta'addanci Zuwa Gida
Dec 15, 2016 04:21Wata Kotu a kasar Kenya ta yanke hukuncin korar Iraniyawa biyu wadan da take tuhuma da ayyukan ta'addanci zuwa gida
-
Shugaban Afirka Ta Kudu Ya Bukaci A Kara Fadada Alaka Ta Tsaro Tsakanin kasarsa Da Iran
Dec 14, 2016 06:30Shugaban kasar Afirka ta kudu Jacob Zuma ya bukaci da a kara fadada alaka ta tsaro tsakanin kasarsa da kuma jamhuriyar muslunci ta Iran.