-
Ghana Ta Sanar Da Tura Sojojinta Zuwa Kasar Senegal Domin Warware Rikicin Siyasar Gambiya
Jan 19, 2017 16:08Shugaban Ghana ya sanar da amincewar kasarsa kan aikewa da sojoji zuwa kasar Senegal domin shiga cikin sahun rundunar hadin gwiwa ta kungiyar bunkasa harkar tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ta ECOWAS da zasu yi amfani da karfi wajen kawar da shugaba Yahaya Jamme'i daga kan karagar mulkin kasarsa.
-
Babban Komandan Sojojin Kasar Gambia Ya Ce Baya Ganin Sojojin Kasar Zasu Shiga Yaki Da Sojojin Yankin Ba
Jan 19, 2017 11:47Babban Komandan sojojin kasar Gambia Usman Baji ya bayyana cewa gwamnatin Gambia ta shiga siyasar cacar baki da kasashen yankin amma yana ganin sojojin kasar ba za su shiga yakin ba.
-
Majalisar Kasar Gambiya Ta Tsawaita Wa'adin Mulkin Yahya Jammeh
Jan 18, 2017 17:32Majalisar dokokin kasar Gambiya ta fitar da wani kuduri na tsawaita wa'adin mulkin shugaban kasar Yahya Jammeh har na tsawon watanni uku da zai fara daga yau Laraba 18 ga watan Janairun nan da muke ciki.
-
Gambia : Jammeh, Ya Ayyana Dokar Ta Baci
Jan 18, 2017 06:21Shugaban Gambia mai barin gado Yahya Jammeh ya ayyana dokar ta baci ta tsawan kwanaki 90 a kasar, a daidai lokacin da ya rage 'yan sa’oi wa’adin mulkinsa ya kare.
-
Zababben Shugaban Gambiya Zai Zauna A Kasar Senegal Har Zuwa Ranar Rantsar Da Shi
Jan 16, 2017 05:48Shugaban kasar Senegal Macky Sall ya amince da bukatar da takwarorinsa shugabannin kasashen Afirka suka gabatar masa na baiwa zababben shugaban kasar Gambiya Adama Barrow mafaka ta siyasa har sai an rantsar da shi a matsayin sabon shugaban kasar Gambiyan a ranar 19 ga watan nan na Janairu.
-
Kungiyar AU Ta Ce Daga 19 Janairu Ba Za Ta Sake Daukar Jammeh A Matsayin Shugaban Gambiya Ba
Jan 14, 2017 18:13Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) ta sanar da cewa daga ranar 19 ga watan Janairun nan da muke ciki ba za ta sake daukar shugaba Yahya Jammeh a matsayin shugaban kasar Gambiya ba don kuwa a wannan ranar ce wa'adin mulkinsa zai kare.
-
Gambiya: Najeriya Na Tattauna Bai wa Shugaba Yahya Jammeh Mafakar Siyasa
Jan 13, 2017 05:41Yan Majalisar Najeriya Suna Tattauna Yiyuwar Bai wa Shugaban Kasar Gambiya Takunkumin Siyasa
-
Shugaba Jammeh Ya Ce Zai Ci Gaba Da Mulki Har Sai Kotun Koli Ta Yanke Hukumcin Karar Da Ya Shigar
Jan 12, 2017 05:34ِDuk da kiraye-kirayen da ake masa na ya sauka daga karagar mulki, shugaban kasar Gambia Yahya Jammeh ya sha alwashin ci gaba da zama zama a kan kujerar mulki har sai kotun kolin kasar ta yanke hukunci dangane da karar da ya shigar inda yake kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasar da aka sanar cewa ya sha kaye.
-
Gambiya: An Dage Ziyarar Shugaban Najeriya Zuwa Gambiya Zuwa Ranar Juma'a:
Jan 11, 2017 19:11An dage tafiyar shugaban kasar Najeriya zuwa Gambiya zuwa jibi Juma'a.
-
Kotun Kolin Gambiya Ta Dage Zaman Sauraren Karar Jammeh Kan Zaben Shugaban Kasa
Jan 10, 2017 17:04Kotun kolin kasar Gambiya ta sanar da dage zaman da ta tsara gudanarwa a yau din nan kan karar da shugaban kasar Yahya Jammeh ya shigar yana kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasar zuwa watan Mayu mai kamawa saboda rashin halartar isassun alkalai.