-
MDD : Harin Da Saudiyya Ta Kaddamar A Hodeida Zai Kara Dagula Al'ammura A Yemen
Jun 13, 2018 14:46Majalisar Dinkin Duniya, ta ce tana ci gaba da tattaunawa domin kaucewa zubar da jini a birnin Hodeida na kasar Yemen, inda kawancen da Saudiyya ke jagoranta ya kaddamar da hari a yau Laraba.
-
UNICEF: Yara Miliyan 11 Ne Ke Bukatar Agaji A Kasar Yamen
Jun 13, 2018 12:32Asusu kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya "UNICEF" ya sanar da cewa: Kananan yara miliyan 11 ne suke bukatar agajin gaggawa a Yamen sakamakon yakin da ke faruwa a kasar.
-
Kira Ga Gwamnatin Sudan Kan Hanzarta Ficewa Daga Rundunar Hadin Guiwar Saudiyya
Jun 11, 2018 12:09Babban sakataren Jam'iyyar Popular Congress Party ta kasar Sudan ya jaddada yin kira ga gwamnatin Sudan kan hanzarta ficewa daga cikin rundunar hadin gwiwar Saudiyya da take yaki a kasar Yamen.
-
Jiragen Saman Yakin Saudiyya Suna Ci Gaba Da Yin Luguden Wuta Kan Kasar Yamen
Jun 07, 2018 18:07Jiragen saman yakin masarautar Saudiyya sun yi luguden wuta kan yankunan lardin Hajjah da ke arewa maso yammacin kasar Yamen.
-
Kawancen Saudia Ta Bukaci Taimakon Amurka Don Kwace Iko Da Birnin Hudaida Na Kasar Yemen
Jun 04, 2018 12:08Kawancin kasar Saudia wadanda suke yakar kasar Yemen sun bukaci taimakon Amurka don kwace iko da birnin Hudaida na bakin ruwa a kasar ta Yemen.
-
Jiragen Saman Yakin Saudiyya Sun Yi Luguden Wuta A Kan Gidajen Fararen Hula A Yamen
Jun 03, 2018 19:07Majiyar asibitin Yamen ta sanar da cewa: Jiragen saman yakin masarautar Saudiyya sun yi luguden wuta kan gidajen fararen hula a lardin Sa'adah da ke arewacin kasar lamarin da ya janyo hasarar rayukan mutane akalla 9.
-
Huthi: Jiragen Yakin HKI Sun Yi Shawagi Kan Garin Hudaida A Kasar Yemen
Jun 03, 2018 12:09Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Abdul Malik Badruddin Al-huthi ya bayyana cewa an ga jiragen yakin HKI suna shawagi a kan garin Hudaida na bakin ruwa a kasar ta Yemen a cikin yan kwanakin da suka gabata.
-
Sojojin Yamen Da Dakarun Sa-Kai Sun Halaka Sojojin Saudiyya Masu Yawa
May 28, 2018 06:24Wasu jerin hare-hare da sojojin Yamen da dakarun sa-kai da suke rufa musu baya suka kaddamar kan sojojin hayar Saudiyya sun kashe da dama daga cikinsu.
-
Saudiyya Ta Sanar Da Mutuwar Sojojinta Biyu A Wani Gumurzu Da Dakarun Yemen
May 27, 2018 17:54Saudiyya ta sanar da cewa wasu sojojin kasar sun mutu a wani gumurzu da suka yi da dakarun kungiyar Ansarullah na kasar Yemen a kan iyakar Saudiyya da Yemen din.
-
Dakarun Yemen Sun Kai Hari Da Makamai Masu Linzami Kan Sansanin Sojin Saudiyya
May 25, 2018 05:24Dakarun kasar Yemen tare da daukin dakarun sa kai na kasar sun kai wani hari kan sansanin sojin kasar Saudiyya da ke Najran da ke kudancin kasar Saudiyyan a matsayin mayar da martani ga ci gaba da har-haren wuce gona da iri da Saudiyyan da kawayenta suke kai wa al'ummar Yemen.