-
Tsoffin Shugabannin Ghana Sun Bukaci A Gudanar Da Zabe Cikin Kwanciyar Hankali
Feb 23, 2016 11:48Tsoffin shugabannin kasar Ghana sun bukaci da a gudanar da zaben shugaban kasa da na 'yan majalisar kasar za a gudanar a kasar cikin kwanciyar hankali sannan kuma bisa inganci ba tare da magudi ba.
-
Zaben Nijar Ya Kai Rana Ta Biyu A Wasu Jihohi Saboda Wasu Matsaloli
Feb 22, 2016 10:59Rahotanni da Jamhuriyar Nijar sun ce an dage gudanar da zaben shugaban kasar da na 'yan majalisu da aka gudanar jiya Lahadi zuwa yau Litinin a wasu jihohi na kasar saboda rashin isar kayan aiki da kuma wasu matsaloli da aka fuskanta.
-
An Fara Zaben Shugaban Kasa Da Na 'Yan Majalisu A Nijar
Feb 21, 2016 10:48An fara gudanar da zaben shugaban kasa da na 'yan majalisu a Jamhuriyar Nijar inda al’ummar kasar za su zabi sabon shugaban kasar cikin 'yan takara 15 da suke fafatawa ciki kuwa har da shugaban kasar mai ci Mahammadu Issoufou wanda ke neman wa'adi na biyu.
-
Shugaba Museveni Ya Lashe Zaben Shugaban Kasar Uganda
Feb 21, 2016 10:46Shugaban kasar Uganda Yoweri Museveni ya lashe zaben shugaban kasar da aka gudanar, lamarin da ya ba shi damar ci gaba da mulkin kasar zuwa shekaru biyar masu zuwa bayan da ya shafe shekaru 30 yana mulkin kasar.
-
An Kawo Karshen Yakin Neman Zaben Da Za'a Gudanar Gobe Lahadi A Nijar
Feb 20, 2016 10:51Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar suna nuni da cewa an kawo karshen yakin neman zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin kasar da za a yi gobe Lahadi a daidai lokacin da dukkanin 'yan takarar suke sanar da fatansu na lashe zaben da za a gudanar din.
-
Zaben Uganda: Shugaba Museveni Na Kan Gaba, Shugaba 'Yan Adawa Kuma Na Tsare
Feb 20, 2016 10:50Rahotanni daga kasar Uganda na nuni da cewa sakamakon farko farko da suke fitowa a zaben shugabancin kasar da aka gudanar na nuni da cewa, shugaban kasar Yoweri Museveni shi ne ke kan gaba, a daidai lokacin da jami'an tsaron kasar suka sake kama madugun 'yan dawar kasar Kizza Besigye.
-
Mutanen Uganda Sun Fara Kada Kuri'a A Zaben Shugaban Kasa A Kasar
Feb 18, 2016 16:42Rahotanni daga kasar Uganda sun bayyana cewar al'ummar kasar sun fara kada kuri’unsu a zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisu da ake gudanarwa a yau din nan Alhamis, da ake ganin shugaban kasar mai ci Yoweri Museveni ne zai lashe zaben.
-
Shugaban Kasar Chadi Idris Deby Ya Nada Sabon Firayi Ministan Kasar
Feb 14, 2016 17:50Shugaba Idriss Deby na kasar Chadi ya nada Pahimi Padacke Albert a matsayin sabon Firaministan kasar biyo bayan murabus din da tsohon firayi ministan kasar Kalezeube Pahimi Deubet yayi.