-
Iran : Zarif Na Halartar Taron Gaggawa Na OIC Kan Kisan Gillan New Zealand
Mar 22, 2019 03:03A yammacin jiya Alhamis ne ministan harkokin wajen kasar Iran, Dakta Muhammad Jawad Zarif ya isa birnin Istanbul na kasar Turkiyya don halartar taron gaggawa na kungiyar hadin kan kasashen musulmi OIC da nufin tattauna harin ta'addancin da aka kai wa masallata a wasu masallatai guda biyu na kasar New Zealand.
-
Ministan Harkokin Wajen Iran Zai Ziyarci Kasar Syria
Mar 06, 2019 02:26Ma’aikatar harkokin wajen Jamhuriyar musulunci ta Iran ta sanar da cewa; ministan harkokin wajen kasar Muhammad Jawad Zarif zai kai ziyara kasar Syria inda zai gana da shugaba Basshar Assad.
-
Zarif: Amurka Ba Za ta Iya Cimma Burinta Na Durkusar Da Kasar Iran Ba
Feb 25, 2019 11:32Ministan harkokin wajen kasar Muhammad Jawad Zarif ya bayyana cewa; gwamnatin Amurka ta dauki dukkanin matakan da take ganin cewa za su iya durkusar da kasar Iran, amma dai ba ta iya cimma burinta ba.
-
Zarif: Babu Wanda Ya Isa Ya Shiga Tsakanin Dangantaka Mai Karfi Tsakanin Iran Da Iraqi
Jan 13, 2019 15:37Ministan harkokin wajen kasar Iran Mohammad Jawad Zarid ya bayya na cewa babu wata kasa wacce ta isa ta bata dangantakar da tsakanin kasashen Iran da Iraqi.
-
Iran Ta Bukaci Kasar Britania Ta Mayarwa Kasar Fam Miliyon 450 Wanda Ta Rike
Dec 31, 2018 08:26Ministan harkokin wajen kasar Iran Mohammad Javad Zareef ya bukaci gwamnatin kasar Britania ta mayarwa kasar Iran kudadenta da ta rike tun bayan nasarar juyin juya halin musulunci a kasar.
-
Zarif: Iran Ba Za Ta Tattauna Da Wata Kasa Kan Makamanta Na Kariya Ba
Dec 05, 2018 13:16Ministan harkokin wajen kasar Iran Dakta Muhammad Jawad Zarif ya bayyana cewar Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba za ta taba tattaunawa da wata kasa dangane da makamanta na kariya ba.
-
Zarif: Kasashen Turai Sun Yi Gum Da Bakunansu Kan Harin 'Yan Ta'adda A Aleppo
Nov 26, 2018 02:04Ministan harkokin wajen kasar Iran Muhammad Jawad Zarif ya yi kakkausar suka, dangane da yadda kasashen yammacin turai suka yi gum da bakunansu kan harin da 'yan ta'adda suka kai da makamai masu guba a kan birnin Aleppo na Syria.
-
Zarif Yayi Watsi Da Barazanar Amurka Na Sanya Al'ummar Iran Cikin Mawuyacin Hali
Nov 11, 2018 13:43Ministan harkokin wajen kasar Iran, Dakta Muhammad Jawad Zarif yayi watsi da barazanar takwararsa na Amurka Mike Pompeo na sanya al'ummar Iran cikin mawuyacin hali, yana mai cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta ci gaba da wanzuwa da kuma kara samun ci gaba duk kuwa da takunkumin Amurka.
-
Zarif: Takunkumin Amurka A Kan Iran Ya Bakanta Sunan Amurka A Duniya
Nov 07, 2018 15:35Ministan harkokin wajen kasar Iran Muhammad Jawad Zarif ya bayyana cewa, takunkumin da Amurka ta sake kakaba wa Iran, ya kara bakanta sunan Amurka a duniya.
-
Zarif: Amurka Ta Zama Saniyar Ware Bayan Ficewa Daga Yarjejeniyar Nukiliya
Aug 16, 2018 13:39Ministan harkokin wajen kasar Iran Muhammad Jawad zarif ya bayyana cewa, Amurka ta mayar da kanta saniyar ware, tun bayan da ta fice daga yarjejeniyar shirin Iran na nukiliya.