-
Senegal : Kotu Ta Bukaci Daurin Shekaru 7 Ga Magajin Birnin Dakar
Feb 17, 2018 11:19Wata kotu a birnin Dakar na kasar Senegal, ta bukaci daurin shekaru bakwai a gidan kaso ga magajin babban birnin Dakar, Khalifa Sall.
-
Nijar : An Rusa Kananan Hukumomi 3
Feb 17, 2018 10:55Gwamnatin Nijar, ta rusa wasu majalisun zababun mashawartan kananan hukumomin guda uku da suka hada da Golle (Jihar Dosso), da Tesker (Jihar Zinder) da kuma na karamar hukumar Dakoro a Jihar Maradi.
-
Masar : An Hallaka Masu Da'awar Jihadi 7 A Yankin Sina
Feb 17, 2018 10:44Rundinar sojin kasar Masar ta sanar da kashe 'yan tada kayar baya bakwai a ci gaba da farmakin data kaddamar a yankin Sina, da nufin tsarkake shi daga duk wata barazanar ta'addanci.
-
Afrika Ta Kudu : Jacob Zuma, Ya Yi Murabus
Feb 15, 2018 02:22Shugaban Afrika ta Kudu, Jacob Zuma, ya sanar da yin murabus daga mulkin kasar, bayan shafe makwanni yana fuskantar matsin lamba daga jam'iyyarsa ta ANC.
-
Jagoran 'Yan Adawa Na Zimbabwe Ya Rasu
Feb 15, 2018 02:21Babbar Jam'iyyar adawa ta (MDC), A Zimbabwe, ta sanar da rasuwar jagoran ta, Morgan Tsvangirai, da yammacin ranar Laraba.
-
Faransa Ta Hallaka Masu Da'awar Jihadi 10 A Mali
Feb 15, 2018 02:21Majiyoyin tsaro a Mali, sun ce a kalla mayakan dake da'awar jihadi goma ne suka hallaka a wani harin sama da na kasa da sojin Faransa suka kai a arewacin Mali.
-
Sabon Zargin Tawagar MDD Da Lalata A (DRC)
Feb 13, 2018 13:11Tawagar MDD dake aikin wanzar da zaman lafiya a Jamhuriyar demokuradiyar Congo ta karbi rahotannin wasu zarge-zargen aikata ba daidai ba, ciki har da wasu laifukan yin lalata guda uku da ake zargin ma'aikatan nata da aikatawa.
-
Afrika Ta Kudu : Zuma Zai Bayyana Matsayinsa Ranar Laraba
Feb 13, 2018 12:55Wasu majiyoyi daga AFrika ta Kudu na cewa, shugaban kasar Jacob Zuma dake fusknatr matsin lamba zai bayyana matsayinsa a gobe Laraba.
-
Kamaru : An Ayyana Dokar Ta Baci A Yankunan 'Yan A Ware
Feb 11, 2018 01:47Gwamnatin Kamaru, ta ayyana dokar ta baki a yankunan masu magana da harshen turancin Ingila, bisa fargabar hare hare na 'yan a ware.
-
Tanzaniya Ta Janye Daga Shirin Taimakawa 'Yan Gudun Hijira
Feb 11, 2018 00:40Kasar Tanzaniya ta sanar da janyewa daga wani shirin Majalisar Dinkin Duniya na taimakawa 'yan gudun hijira.