-
'Yan Sandan Nijeriya Sun Ce Suna Neman Sanata Dino Melaye Ruwa A Jallo
Mar 28, 2018 11:42Rundunar 'yan sandan Nijeriya ta sanar da cewar tana neman Sanata Dino Melaye, dan majalisar tarayya daga jihar Kogi tare da dan tsohon gwamnan jihar Kogin Muhammad Audu saboda zarginsu da ake yi da ba da bayanan karya ga 'yan sanda.
-
Tashin Gobara A Sansanin 'Yan Gudun Hijira A Nigeriya Ya Lashe Rayukan Mutane
Mar 27, 2018 07:22Bullar gobara a sansanin 'yan gudun hijira da ke garin Rann a jihar Borno a shiyar arewa maso gabashin Nigeriya ta lashe rayukan mutane akalla biyar tare da raba wasu daruruwa da matsugunansu.
-
An Samu Raguwar Yaduwar Cutar Lassa A Najeriya
Mar 27, 2018 01:19Hukumar lafiya ta duniya ta ce an fara samun raguwar yaduwar cutar zazzabin Lassa a Najeriya.
-
Najeriya : An Mika 'Yan Matan Dapchi Ga Hannun Iyayensu
Mar 25, 2018 13:46Hukumomi a Najeriya sun mika 'yan matan nan na makarantar sakandaren Dapchi a hannun iyayensu a yau Lahadi.
-
Sojojin Nijeriya Sun Bude Hanyar Maiduguri-Bama-Banki Dake Hannun B/Haram Na Tsawon Shekaru
Mar 24, 2018 12:30Sojojin Nijeriya sun gudanar da bikin bude hanyar Maiduguri-Bama-Banki da ke jihar Borno a yau din nan Asabar shekaru hudu bayan da 'yan kungiyar ta'addancin nan ta Boko Haram suka kwace hanyar, lamarin da mutanen yankin suka yi maraba da shi.
-
Najeriya : 'Yan Matan Makarantar Dapchi 101 Boko Haram Ta Sako
Mar 21, 2018 12:32Gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa 'yan matan makarantar sakadaren Dapchi 101 ne kawo yanzu kungiyar Boko Haram ta sako daga cikin 110 da kungiyar ta yi garkuwa dasu.
-
Najeriya: An Sako Wasu Daga Cikin 'Yan Matan Dapchi A Yau Laraba
Mar 21, 2018 08:27Rahotanni daga Najeriya na cewa an sako wasu daga cikin 'yan matan Dapchi da mayakan Boko Haram suka sace.
-
'Yan Sandan Nijeriya Sun Zargi Dino Melaye Da Raba Makamai Don Tada Hankali
Mar 20, 2018 02:20Rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta gabatar da wasu matasa da ta kama bisa zargin suna da alaka da wata kungiyar ‘yan ta’adda da suke gudanar da ayyukansu a jihar Kogi wadanda suka ce dan majalisar dattawan Nijeriyan Sanata Dino Melaye ne ke ba su makamai.
-
Najeriya: Shugaba Buhari ya fasa zuwa Rwanda
Mar 19, 2018 15:28Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya fasa zuwa kasar Rwanda domin halartar wani taron shugabanin Tarayyar Afrika kan yarjejeniyar kasuwanci.
-
Buhari Ya Gana Da Shugabannin Majalisun Nijeriya Don Dinke Barakar Da Ta Kunno Kai
Mar 16, 2018 07:39A wani abin da ake gani a matsayin kokarin dinke barakar da ta kunno kai tsakanin fadar shugaban Nijeriya da majalisun kasar, shugaba Muhammadu Buhari na Nijeriyar ya gana da shugabannin majalisun tarayyar kasar su biyu a daren jiya.