-
Syria : Dakarun Kurdawa 28 Suka Hallaka A Hare-haren Turkiyya
Apr 26, 2017 06:36Hukumar dake sa ido kan al'amuran kare hakkin bil adama ta kasa a Syria ta ce adadin mutanen suka rasa rayukansu a hare-haren da jiragen saman Turkiyya kan dakarun Kurdawa ya kai 28, kana wasu 19 na daban suka raunana.
-
Syria Na Shirye Don Tsagaita Wuta A Khan Cheikhoun
Apr 25, 2017 01:10Ministan tsaron Rasha ya sanar da cewa dakarun kasar Syria a shirye suke domin tsagaita wuta a Khan Cheikhoun domin baiwa kwararu na kasa da kasa damar shiga yankin don aiwatar da bincike kan zargin amfani da iskar gas mai guba.
-
Rasha A Shirye Take Ta Tura Da Sojojin Kasanta Cikin Siriya Don Fada 'Yan Ta'adda
Apr 24, 2017 12:43Majiyoyin sojin kasar Siriya sun bayyana cewar Rasha ta sanar da gwamnatin kasar Siriya cewa a shirye take ta tura da sojojinta na kasa zuwa kasar Siriyan don taimakawa gwamnatin a fadar da take yi da 'yan ta'addan takfiriyya da suke samun goyon bayan kasashen waje.
-
Sergei Lovrov Ya Ce; Rasha, Iran Da Kungiyar Hizbullahi Suna Yaki Da Ta'addanci Ne A Siriya
Apr 23, 2017 00:54Ministan harkokin wajen kasar Rasha ya jaddada bukatar ganin kasashen yammacin Turai da Amurka sun canja ra'ayinsu kan kasar Siriya domin samun nasarar murkushe 'yan ta'adda a cikin kasar.
-
Rahoton Kwamitin Bincike Na MDD Kan Amfani Da Sanadarai Masu Guba A Syria
Apr 22, 2017 13:04Kwamitin bincike da hukumar hada yaduwar makamai masu guba ta majalisar dinkin duniya ta kafa domin yin bincike kan amfani da sanadarai masu guba a Syria, ya fitar da rahotonsa na farko.
-
Shugaba Asad Ya Zargi Turkiyya Da Ba Wa 'Yan Ta'adda Makamai Masu Guba
Apr 22, 2017 01:16Shugaban kasar Siriya Bashar al-Asad yayi kakkausar suka ga kasar Turkiyya saboda ba wa 'yan ta'addan takfiriyya da suke yaki a kasar Siriyan makamai masu guba yana mai cewa ba shi da komai kashin shakku dangane da hadin gwiwan da ke tsakanin gwamnatin Turkiyya da 'yan ta'addan.
-
Jinkirin MDD Na Yin Allah Wadai Da Harin Ta'addancin Da Aka Kai Kasar Siriya
Apr 21, 2017 00:04Bayan jan kafa na wani lokaci, daga karshe dai kakakin kwamitin kolin kula da hakkokin bil-Adama na Majalisar Dinkin Duniya ya fito ya yi tofin Allah tsine kan harin ta'addancin da aka kai wa tawagar fararen hula a kasar Siriya.
-
Hukumar "UNICEF" Ta Bukaci Daukan Matakin Kare Kananan Yara A Kasar Siriya
Apr 17, 2017 01:22Asusun Kula da Kananan Yara da Mata na Majalisar Dinkin Duniya "UNICEF" ta bukaci duniya ta dauki matakin kare kananan yara daga irin masifar da suke fuskanta a kasar Siriya.
-
Sharhi : Zaman Ministocin Harkokin Wajen Rasha, Iran, Da Syria A Moscow
Apr 16, 2017 15:00A ranar Juma’a da ta gabata ce ministocin harkokin wajen kasashen Rasha, Iran, da kuma Syria, suka gudanar da wani zama a birnin Moscow na kasar Rasha, domin tattaunawa kan batun harin da Amurka ta kaddamar a kan kasar Syria.
-
Syria: An Sami Karuwar Wadanda Su ka Rasa Rayukansu A Harin Ta'addanci.
Apr 16, 2017 04:50Kawo ya zuwa yanzu wadanda harin ta'addanci a gundumar Halab ya rutsa da su sun kai 110.