Kungiyar 'Yan ta'adda ta Boko Haram sun kai hari akan sansanoni biyu na sojojin kasar dake Jahar Borno a arewa maso gabashin kasar
Sojojin Najeriya sun sanar da cewa; 'yan kungiyar ta Boko haram suna tilastawa fararen hula ficewa daga gidajensu da garuruwansu a yankin arewa maso gabacin kasar
Majiyar hukumar kare hakkin bil'adama ta Majalisar dinkin duniya a tarayyar Najeriya ta bada sanarwan cewa mutane akalla dubu 30 ne suka kauracewa gidajensu a garin Baga dake gabacin Jihar Borno a arewa maso gabacin kasar.
Rundinar sojin kasar Nijar ta kaddamar da wani gagarimin farmaki data kai kan 'yan ta'addan boko haram a yankin tafkin Chadi, inda ta hallaka 287 daga cikinsu a cewar wata sanarwa da ma'aikatar tsaron kasar ta fitar a jiya Laraba.
Rundunar sojin sama ta Najeriya ta ce ta fatataki 'yan Boko Haram a garin Baga dake jihar Borno a arewa maso gabashin kasar.
Shuwagabannin kasashe mambobin kwamitin tafkin Chadi, cewa da (CBLT), sun sha alwashin ganin bayan kungiyar Boko haram domin kawo karshen tsatsauran ra'ayi a yankin.
Kungiyar kare hakkin bil adama ta kasa da kasa Amnesty International, ta bukaci kotun hukunta manyan laifuka ta duniya cewa da ICC, tada binciki lamarin kisan-kiyashin da kungiyar Boko ta aikata tun bayan kafuwarta.
A Kamaru, an kafa wani kwamitin kasa da aka aza wa yaunin karbar makaman yaki a yankunan dake fama da rikici da suka hada da yankin arewa mai nisa da kuma na masu magana da turancin Ingilishi.
Kungiyar Tarayyar Turai (EU) da kuma kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ta ECOWAS sun bayyana tsananin damuwarsu dangane da yadda kungiyar ta'addancin nan ta Boko Haram take kara zafafa hare-haren da take kai wa yankunan arewa maso gabashin Nijeriya.
Rundunar sojin Nijeriya ta bayyana cewar sojoji 23 ne aka kashe a harin da 'yan Boko Haram suka kai wani sansanin sojojinta da ke gariin Metele na jihar Borno ranar 18 ga watan Nuwamba nan sabanin wasu rahotanni da suke cewa sama da sojoji 100 ne aka kashe yayin harin.