-
Trump: Ba Za'a Sake Sakin Wani Fursuna Daga Gidan Yarin Guantanamo Ba
Jan 04, 2017 05:53Shugaban Amurka mai jiran gado Donald Trump ya sanar da adawarsa ga rufe gidan yarin nan na Guantanamo yana mai cewa ba za a sake sakin wani fursuna daga gidan yarin da Amurka take tsare da fursunonin da take zargi da ayyukan ta'addanci ba.
-
Trump Ya Zargi Obama Da Yin Kafar Angulu A Shirin Mika Masa Mulki
Dec 29, 2016 06:59Zababben shugaban kasar Amurka mai jiran gado Donald Trump ya zargi shugaban kasar mai barin gado Barack Obama, da kawo tarnaki a shirye-shiryen mika masa mulkin Amurka.
-
'Yan Kungiyoyin Fararen Hular Bahrain Sun Yi Gangami A Gaban Otel Din Trump a Birnin Washington
Dec 08, 2016 18:13Yan kungiyoyin farar hular Bahrain sun taro gaban Otel din Donald Trump zababben shugaban Amurka a birnin Washington
-
Mutanen New York Na Ci Gaba Da Nuna Rashin Amincewa Da Zaman Trump A Garin
Dec 07, 2016 17:07Rahotanni daga birnin New York na Amurka na nuni da cewa dubun dubatan mutanen garin ne suka sanya hannu kan wata takarda don nuna rashin amincewarsu da ci gaba da zaman shugaban Amurka mai jiran gado Donald Trump a garin saboda irin kudin da ake kashewa wajen tsaronsa.
-
Kasar China Ta Nuna Fushinta Da Tattaunawar Trump Da Shugabar Taiwan
Dec 03, 2016 18:04Kasar China ta bayyana tsananin fushinta dangane da tattaunawa ta wayar tarho da zababben shugaban Amurka Donald Trump yayi kai tsaye da shugabar kasar Taiwan, da take kallon wajen a matsayin wani yanki na kasar China da ya balle.
-
Ganawar Ministan harakokin wajen Masar da Mataimakin Trump
Dec 01, 2016 11:46Ministan Harakokin wajen Masar da Mataimakin sabon Kasar Amurka sun tattauna kan fadada alaka da aiki tare tsakanin kasashen biyu.
-
Rikici Ya Kunno Kai Cikin Kwamitin Karbar Mulki Na Donald Trump
Nov 16, 2016 11:20Rahotanni daga Amurka suna nuni da cewa tun ba a je ko ina ba an fara samun baraka cikin kwamitin karbar mulki da zababben shugaban kasar Amurka Donald Trump ya kafa inda wasu daga cikin kusoshin tawagar suka fara yin murabus sannan kuma ake ta kace nace dangane da irin rawar da iyalansa Mr. Trump din za su taka a wannan fagen.
-
Jagora Imam Khamenei: Sakamakon Zaben Amurka, Ba Shi Da Wani Bambanci A Wajenmu
Nov 16, 2016 11:20Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bayyana cewar Iran dai ba ta cikin wata damuwa dangane da sakamakon zaben kasar Amurka, to sai dai tana cikin shirin fuskantar koma mai zai faru, yana mai cewa sakamakon zaben ba shi da wani bambanci a wajen Iran.
-
Amurkawa Na Ci Gaba Da Zanga-Zangar Kin Jinin Donald Trump A Garuruwa Daban-Daban Na Kasar
Nov 12, 2016 16:49Rahotanni daga Amurka na nuni da cewa ana ci gaba da karuwar mutanen da suke fitowa kan tituna daban-daban na kasar da nufin ci gaba da gudanar da zanga-zangar adawa da nasarar da Donald Trump ya samu a zaben shugaban kasar da aka gudanar a kwanakin baya.
-
Shafin Donald Trump Ya Cire Wasu Kalaman Batunci Kan Musulmi
Nov 10, 2016 15:40Masu kula da shafin yanar gizo na Donald Trump zabebben shugaban kasar Amurka sun cire irin kalaman batuncin da ya rika yi a kan musulmi daga shafin nasa.