-
Kwamandan Sojin Amurka Ya Nuna Damuwa Kan Tasirin Kasar Iran A Yankin Gabas Ta Tsakiya
May 22, 2018 14:50Babban kwamandan rundunar sojin Amurka ya ce rawar da Jamhuriyar Musulunci ta Iran take takawa a yankin gabas ta tsakiya tana barazana ga manufofin Amurka a yankin.
-
Sojojin Siriya Sun Karbe Daukacin Birnin Damascos Da Gewayensa
May 21, 2018 09:52Rundinar sojin Siriya ta sanar da karbe daukacin ikon birnin Damascos da gewayensa, bayan da sojojin gwamnatin kasar suka kwato tunga mafi girma da 'yan ta'adda na IS ke rike da a kudancin babban birnin kasar.
-
Iran Ba Ta Fatan Wani Sabon Rikici A Yankin_Rohani
May 11, 2018 01:11Shugaban Jamhuriya Musulinci ta Iran, Hassan Rohani, ya bayyana cewa kasarsa bata fatan barkewar wani sabon rikici a gabas ta tsakiya .
-
Rasha : Putin Ya Gana Da Netanyahu A Moscow
May 09, 2018 11:07Shugaban kasar Rasha, Vladimir Putin ya ce yana nazarin samar da mafita a gabas ta tsakiya tare da fira ministan Isra'ila Benjamin Netanyahu.
-
Sojojin Siriya Sun Tsarkake Yankin Duma_ Rasha
Apr 12, 2018 10:01Ma'aikatar tsaron Rasha ta sanar da cewa, sojojin gwamnatin Siriya sun kwace ikon Duma, gari na karshe dake hannun 'yan tada kayar baya a yankin gabashin Ghouta.
-
Gaza : Sojojin Isra'ila Sun Kashe Palasdinawa 5
Apr 06, 2018 12:32Rahotanni daga zirin Gaza na cewa, Palasdinawa 5 ne sukayi shahada sakamakon harbin bindiga da sojojin yahudawan mamaya na sahayoniya suka masu a ci gaba da zanga zangar da suke kan iyakar yankin da Is'ra'ila.
-
Duniya Ta Taimaka Wa Labanon Da Dala Bilyan 11
Apr 06, 2018 11:35Kasashen duniya da suka taru a birnin Paris na kasar Faransa, sun alkawarta taimaka wa kasar Labanon da tallafin kudi da ya kai dalar Amurka sama Bilyan 11.
-
Siriya : An Fara Kwashe 'Yan Tada Kayar Baya A Yankin Ghouta
Mar 23, 2018 01:21A karon farko tun bayan farmakin da dakarun Siriya ke kaiwa a yankin gabashin Ghouta, wani ayarin motocin 'yan tada kayar baya ya fice daga yankin.
-
Afganistan : Harin Ta'addanci Ya Kashe Mutum 26 A Kabul
Mar 21, 2018 14:43Rahotanni daga Afganistan na cewa mutane a kalla 26 ne galibi samari suka rasa rayukansu a wani harin kunar bakin wake da kungiyar 'yan ta'adda ta IS ta dauki alhakin kaiwa a Kabul babban birnin kasar.
-
Siriya : Turkiyya Ta Kwace Yankin Afrin
Mar 19, 2018 03:45Dakarun Turkiyya da mayakan Siriya dake samun goyan bayan Ankara sun kwace daukacin ikon birnin Afrin tungar mayakan kurdawa da Turkiyyar ke kallo a matsayin 'yan ta'adda.