-
Sabon Shugaban Kasar Gambia Ya Bukaci A Binciki Yahya Jammeh
Jan 25, 2017 07:35Sabon shugaban kasar Gambia Adama Barrow ya bukaci a binciki Yahya Jammeh tsohon shugaban kasar kan zarginsa da wawushe miliyoyin daloli daga baitulmalin kasar.
-
'Yan Gudun Hijira Gambia Sun Fara Komawa Gida
Jan 24, 2017 18:22Kimanin mutanen Gambia 8,000 ne da sukayi gudun hijira domin kaucewa rikicin siyasa kasar ne suka koma gida bayan da tsohon shugaban kasar Yahya Jammeh ya fice daga kasar.
-
Sojojin ECOWAS Za Su Ci Gaba Da Zama A Gambiya Don Binciko Makaman Da Aka Boye
Jan 24, 2017 11:21Shugaban kungiyar tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS), Marcel de Souza ya ce dubun dubatan sojojin kungiyar kasashen ECOWAS za su ci gaba da zama a kasar Gambiya har na tsawon lokaci don ci gaba da binciko makaman da aka boye da kuma tabbatar da zaman lafiya da tsaron kasar.
-
Gambiya: Sabon Shugaban Kasar Gambiya Ya Bukaci Sojojin Ecowas Su Ci gaba Da Zama A Kasar.
Jan 23, 2017 19:01Sabon shugaban na Gambiya Adama Barrow, yana Son ganin cewa dakarun Ecowas sun ci gaba da zama a kasar har sai harkokin tsaro sun dawo.
-
Sabon Shugaban Gambiya Yayi Karin Bayani Kan Dalilan Da Suka Bar Yahya Jammeh Ya Bar Kasar
Jan 23, 2017 11:10Sabon shugaban kasar Gambiya Adama Barrow yayi karin haske dangane da dalilan da ya sanya ya bari aka fita da tsohon shugaban kasar Yahya Jammeh daga kasar da kuma batun wa'adin mulkinsa.
-
Sabon Shugaban Gambiya Ya Ce: Tsohon Shugaban Kasar Yahya Jammeh Ya Kwashe Dukiyar Kasar
Jan 23, 2017 07:06Sabon shugaban kasar Gambiya ya yi da'awar cewa: Tsohon shugaban kasar ta Gambiya Yahya Jammeh ya kwashe dukkanin dukiyar baitul -malin kasar kafin fitarsa zuwa gudun hijira.
-
A Yau Ne Ake Sa Ran Yahya Jammeh Zai Bar Kasar Gambiya
Jan 21, 2017 11:52A wani lokaci a yau ne ake sa ran tsohon shugaban kasar Gambiya Yahya Jammeh zai bar birnin Banjul, babban birnin kasar ta Gambiya tare da shugaban kasar Guinea Alpha Conde don fara gudun hijira a wajen kasar bayan da ya amince zai sauka daga mulkin kasar.
-
Tawagar ECOWAS Na Tattaunawar Karshe Da Jammeh
Jan 20, 2017 17:22Tawagar kungiyar ECOWAS da ta kunshi shugaban Guinea Conakry Alpha Conde, da takwaransa na Mauritania Mohamed Ould Abdoul Aziz, ta isa birnin Banjul na kasar Gambia a yunkurin shawo kan Yahya Jammeh ya mika ragamar mulki a hannun Adama Barrow a wannan rana ta juma’a.
-
Kungiyar ECOWAS Ta Ba Wa Yahya Jammeh Dama Ta Karshe Kafin Sojoji Su Shigo
Jan 20, 2017 11:04Kungiyar kasashen Yammacin Afirka ECOWAS ta sanar da cewa ta dakatar da sojojin kasar Senegal daga shiga kasar Gambia, domin bayar da damar sake tattaunawa da shugaba Yahya Jammeh dangane da batun sauka daga mulkin kasar bayan wa'adinsa ya kare.
-
Komitin Tsaro Na Majalisar Dinkin Duniya Ya Amincewa Kasashen ECOWAS Shiga Cikin Lamuran Gambia
Jan 20, 2017 03:32A Jiya da yamma ne wakilan komitin tsaro na majalisar dinkin duniya gaba dayansu suka amincewa kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS da suka dauki matakin da suka ga ya dace na saura shugabanci a kasar Gambia.