-
Mali : Adadin Fulanin Da Aka Kashe Ya Kai 160
Mar 25, 2019 22:29A Mali, adadin fulanin da aka kashe a kauyen Ogossagou dake jihar Mopti a tsakiyar kasar ya kai 160, a yayin da kuma wasu majiyoyi ke cewa adadin zai iya wuce ma hakan.
-
Mali : Mata Da Diyan Sojoji Sunyi Zanga zanga
Mar 23, 2019 01:49A Kasar Mali, ‘yan uwa da mata da kuma diyan sojojin kasar ne sukayi zanga zanga a biranen Segu da Sevare dake tsakiyar kasar domin nuna bacin ransu akan yawaitar kashe kashen sojojin kasar a hare haren ta'addanci.
-
'Yan Bindiga Sun Kashe Sojojin Mali 16
Mar 17, 2019 15:09Wasu ‘yan bindiga sun kai hari akan wani sansanin sojan Mali da yake a tsakiyar kasar tare da kashe sojoji 16.
-
An Hallaka Sojoji 6 A Kasar Mali
Mar 13, 2019 13:28Rundunar tsaron kasar Mali ta sanar da mutuwar sojojinta shiga sanadiyar tashin Nakiya a tsakiyar kasar
-
Mali : An Kashe Fararen Hula 17
Feb 28, 2019 02:51Majiyar tsaron kasar Mali ta sanar da kisan fararen hula 17 a tsakiyar kasar
-
Sojojin Somalia Sun Kwace Iko Da Wasu Kauyuka Daga Hannun Alshabab
Feb 25, 2019 11:34Dakarun kasar Somalia sun samu nasarar kwace wasu kauyuka biyu daga hannun mayakan ‘yan ta’addan Al-shabab.
-
An Kashe Sojojin MDD 3 A Kasar Mali
Feb 25, 2019 02:16Ma'aikatar tsaro da kare fararen hula a kasar Mali ta bada sanarwan cewa an kashe sojojin tabbatar da zaman lafiya uku a tsakiyar daren jaumma'an da ta gabata.
-
Ana Samun Galaba A Yaki Da Ta'addanci A Yankin Sahel_Faransa
Feb 23, 2019 12:57Firaministan Faransa, Edouard Philippe, ya bayyana cewa ana samun galaba a yakin da ake da mayakan dake ikirari da sunan jihadi da kuma matalsar tsaro a yankin sahel.
-
Mali : Yawan 'Yan Gudun Hijira Ya Linka Sau Uku
Feb 01, 2019 00:55Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa yawan 'yan gundun hijira a Mali, ya linka har sau uku a cikin shekara guda, saboda matsalar tsaro a iyakar kasar da Burkina Faso.
-
Mali : (AU) Ta Yi Allah Wadai Da Hari Kan Tawagar MINUSMA
Jan 23, 2019 07:28Shugaban hukumar gudanarwar kungiyar tarayyar Afirka (AU), Moussa Faki Mahamat, ya yi Allah wadai da kakkausar murya kan harin da ya kashe sojojin kasar Chadi 10 dake aikin kiyaye zaman lafiya karkashin tawagar MINUSMA a kasar Mali.