-
Gwamnatin Masar Ta Kara Wa'adin Gudanar Da Dokar Ta Baci A Lardin Sina Ta Arewa Na Kasar
Jan 13, 2018 03:03Gwamnatin Masar ta sanar da cewa: Za a ci gaba da gudanar da dokar ta baci a lardin Sina ta Arewa da nufin dakile bullar ayyukan ta'addanci a yankunan.
-
Sudan Tana Sanya Idanu Akan Kai Da Komowar Sojojin Masar Da Eritrea
Jan 12, 2018 08:26Mataimakin Shugaban Kasar Sudan Ibrahim Mahmud ne ya sanar da haka yana mai bayyana kai da komowar sojojin makwabtan nasu biyu a matsayin barazana ta tsaro ga Sudan.
-
Kotu A Masar Ta Rusa Hukuncin Da Aka Zartar Kan Tsohon Ministan Harkokin Cikin Gidan Kasar
Jan 11, 2018 15:23Kotun daukaka kara a Masar ta rusa hukuncin da wata kotu a birnin Alkahira ta zartar kan tsohon ministan harkokin cikin gidan kasar a zamanin mulkin Husni Mubarak.
-
Masar: An Yanke Wa 'Yan Kungiyar Ikhwan 23 Zaman Kurkuku Na Rai Da Rai
Jan 09, 2018 15:47Wata kotun kasar ta Masar ce ta yanke hukuncin ga mambobin kungiyar ta ikhwan 23 bisa samun su da laifin a rikicin dandalin "Tahrir"a 2013
-
Gwamnatin Sudan Ta Sake Shigar Da Karar Kasar Masar A Gaban Majalisar Dinkin Duniya
Jan 09, 2018 03:04Gwamnatin Sudan ta sake gabatar da kokenta kan kasar Masar a gaban Majalisar Dinkin Duniya tana neman a tilastawa mahukuntan Masar janyewa daga yankunan Sudan da suka mamaye.
-
An Hallaka 'Yan Ta'adda A Gabashin Lardin Al-Arish Na Masar
Jan 08, 2018 15:44Majiyar Tsaron Kasar Masar ta sanar da hallaka wani adadi na 'yan ta'adda a wani sumame da sojojin kasar suka kai a lardin gashin Al-Arish dake jihar Sinai ta arewa.
-
Gwamnatin Masar Ta Karyata Zargin Goyon Bayan Shirin Donald Trump Na Kwace Birnin Qudus
Jan 07, 2018 16:04Gwamnatin Masar ta karyata rahoton da wata jaridar Amurka ta yada cewa: Masar ta nuna yardarta a fakaice da shirin shugaban kasar Amurka na shelanta birnin Qudus na Palasdinu a matsayin fadar mulkin gwamnatin Haramtacciyar kasar Isra'ila.
-
Sudan Ta Rufe Kan Iyakarta Da Kasar Eritrea
Jan 07, 2018 03:09Rufe kan iyakar da Eritrea ya zo ne a daidai lokacin da gwamnatin Khartum ta kafa dokar ta baci a jahar Kassala da ke kan iyaka.
-
An Kai Hari Kan Wani Ofishin Yansanda A Kasar Masar
Jan 06, 2018 15:36Majiyar jami'an tsaro a kasar Masar ta bayyana cewa wasu yan adawa sun kai hari kan wani ofishin yansanda a gabacin birnin Alkahira a yau Asabar.
-
Sudan Ta Aike Da Dubban Sojoji Zuwa Kan Iyakokinta Da Eritrea
Jan 06, 2018 03:03Rundunar Sojin Sudan ta aike da duban sojoji zuwa yankunan dake kan iyakokin kasar da kasar Eritrea.