An Kai Hari Kan Wani Ofishin Yansanda A Kasar Masar
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i27075-an_kai_hari_kan_wani_ofishin_yansanda_a_kasar_masar
Majiyar jami'an tsaro a kasar Masar ta bayyana cewa wasu yan adawa sun kai hari kan wani ofishin yansanda a gabacin birnin Alkahira a yau Asabar.
(last modified 2018-08-22T11:31:15+00:00 )
Jan 06, 2018 19:06 UTC
  • An Kai Hari Kan Wani Ofishin Yansanda A Kasar Masar

Majiyar jami'an tsaro a kasar Masar ta bayyana cewa wasu yan adawa sun kai hari kan wani ofishin yansanda a gabacin birnin Alkahira a yau Asabar.

Kamfanin dillancin labaran AFP na kasar Faransa ya nakalto wata majiya ta yansanda a birnin Alkahira yana cewa wasu gungun yan adawa da gwamnatin kasar sun kai harin ne bayan mutuwar wani dan adawa a tsare a hannun jami'an tsaron. Gungun yan adawar sun kona motocin yansanda sannan sun doshi wasu manya manyan gine-gine na jami'an tsari a yankin ne sai yansandan suka tarwatsau da hayaki mai sa hawaye. 

Majiyar ta kara da cewa mutane 9 ne suka ji rauni daga cikinsu har da jami;an yansanda biyu a lokacin fafatawan da yan adawar suka yi da yansanda a yanlin Al-Maqtam na gabacin birnin Alkahira. Jami'an tsaron dun kama mutane 20 daga cikin mutanen.

Majiyar ta kammala da cewa a jiya jumma ce wani matashin da jami'an tsaron suka kama da zargin sauda miyagun kwayoyi ya muto sanadiyyar azabtarwa a ofishin yansandan.