Sudan Ta Rufe Kan Iyakarta Da Kasar Eritrea
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i27081-sudan_ta_rufe_kan_iyakarta_da_kasar_eritrea
Rufe kan iyakar da Eritrea ya zo ne a daidai lokacin da gwamnatin Khartum ta kafa dokar ta baci a jahar Kassala da ke kan iyaka.
(last modified 2018-08-22T07:01:15+00:00 )
Jan 07, 2018 03:09 UTC
  • Sudan Ta Rufe Kan Iyakarta Da Kasar Eritrea

Rufe kan iyakar da Eritrea ya zo ne a daidai lokacin da gwamnatin Khartum ta kafa dokar ta baci a jahar Kassala da ke kan iyaka.

gwamnan jahar ta Kassala Adam Jema ya bada umarni da dakatar da zirga-zirga akan dukkanin hanyoyin da ke isa kasar Eritrea, bisa dogaro da umarnin shugaban kasar Umar Hassan al-Bashir na kafa dokar ta baci.

Gwamnan jahar ta Kassala ya kuma ce; Sojoji sun isa cikin jahar ne domin karbe makamai daga hannun mutane da kuma fada da masu fasakwaurin mutane da kayan masarufi.

A gefe daya, wasu kafafen watsa labaru sun ambaci cewa Masar ta aike da sojojinta zuwa kasar Eritrea a wani abu da yake nuni da kamarin alaka da Sudan.

Alaka a tsakanin Masar da Sudan ta yi kamari saboda sabanin da suke da shi akan hakkin mallakar tsibiran Halayib, da a yanzu yake  karkashin ikon Masar. Tuni dai Sudan ta kira yi jakadanta daga kasar Masar domin yin shawara.