-
Gamayyar Jam'iyyun Adawa A Zambia Ta Bukaci A Sake Kidaya Kuri'un Wasu Yankuna
Aug 15, 2016 13:26Kawancen jam'iyyun adawa akasar Zambia ya bukaci da a sake kidaya kuri'un da aka kada a wasu yankuna, musamman a birnin Lusaka fadar mulkin kasar, bisa zargin gwamnati da tafka magudi.
-
Ana Jiran Sakamakon Zaben Shugaban Kasa Da 'Yan Majalisa A Kasar Zambiya
Aug 12, 2016 05:00Al'ummar kasar Zambiya na ci gaba da jiran dakon sakamakon zaben shugaban kasa da na 'yan majalisar kasar da aka gudanar a jiya Alhamis a zaben da ake kankankan tsakanin shugaban kasar Edgar Lungu da abokin hamaiya Hakainde Hichilema da ke zargin shugaban da lalata tattalin arzikin kasar.
-
Karuwar Rashin Amincewa Da Donald Trump Tsakanin 'Yan Jam'iyyar Republican Ta Amurka
Aug 10, 2016 05:46Rahotanni daga Amurka suna nuni da ci gaba da karuwar masu adawa da dan takaran jam'iyyar Republican a zaben shugaban kasar Amurka da za a gudanar a wannan shekara ta 2016 Donald Trump a tsakanin 'yan jam'iyyar Republican din sakamakon mahanga da kuma irin maganganunsa.
-
Jam'iyyar ANC Mai Mulki Na Kan Gaba A Zaben Afirka Ta Kudu
Aug 04, 2016 11:07Rahotanni daga kasar Afirka ta kudu suna nuni da cewa jam'iyyar ANC mai mulki a kasar ita ce take kan gaba a zaben kananan hukumomin da ake gudanarwa a kasar duk kuwa da cewa akwai yiyuwar ta rasa wasu garuruwan a karon farko tun bayan da ta dare karagar mulki.
-
Hillary Clinton Ta Zama 'Yar Takarar Jam'iyyar Democrats A Zaben Shugaban Amurka
Jun 08, 2016 05:39Rahotanni daga Amurka sun bayyana cewar tsohuwar sakatariyar harkokin wajen kasar Hillary Clinton ta zama 'yar kakarar Jam'iyyar Democrats a zaben shugaban Amurkan da za a gudanar bayan ta samu adadin kuri'un da ake nema ta lashe zaben fidda gwanin dan takarar shugabancin Amurka a karkashin jam'iyyar Democrat din.
-
'Yan Adawan Nijar Sun Sanar Da Aniyarsu Ta Tattaunawa Da Shugaban Kasar
Mar 29, 2016 04:43'Yan adawa a Jamhuriyar Nijar sun sanar da aniyarsu ta zama teburin tattaunawa da shugaban kasar Mahamadou Issoufou bayan da suka kaurace da zagaye na biyu na zaben shugaban kasar da aka gudanar a kwanakin baya.
-
An Tabbatar Da Mutuwar Mutane 4 A Zaben Jihar Rivers, Nijeriya
Mar 21, 2016 10:11Rundunar 'yan sandan Nijeriya ta tabbatar da mutuwar mutane 4 a jihar Rivers biyo bayan rikicin da ya barke a zaben cikin gurbin 'yan majalisun dokokin da aka gudanar a jihar a shekaran jiya Asabar.
-
Firayi Ministan Benin Lionel Zinhou Ya Amince Da Shan Kaye A Zaben Kasar
Mar 21, 2016 09:54Rahotanni daga kasar Jamhuriyar Benin sun bayyana cewar firayi ministan kasar kuma dan takaran jam’iyya mai mulkin a kasar Lionel Zinhou ya amince da shan kaye a zagaye na biyu na zaben shugaban kasar da aka gudanar.
-
Hamma Amadou Zai Shiga Zagaye Na Biyu Na Zaben Niger
Mar 12, 2016 08:59Lauyan jagoran 'yan adawa a Nijar Hama Amadou, Mossi Boubacar ya sanar da cewa Hama Amadou zai shiga zaben shugaban kasar zagaye na biyu da za a gudanar a ranar 20 ga watan Maris din nan sabanin sanarwar da aka yi a baya na cewa ba zai tsaya din ba.
-
Shugaban Angola Ya Ce Zai Sauka Daga Karagar Mulkin Kasar
Mar 12, 2016 08:56Shugaban kasar Angola Jose Eduardo dos Santos ya sanar da cewa ya kuduri aniyar sauka daga karagar mulkin kasar a shekara ta 2018 lokacin da wa'adin mulkinsa zai kare bayan ya shafae kusan shekaru 40 yana mulkin kasar.