-
Gwamnatin Angola Ta Kori Jami'an Diplomasiyyanta Biyu Saboda Batun Halartar Bude Ofishin Jakadancin Amurka A Qudus
May 23, 2018 13:05Ministan harkokin wajen kasar Angola, Manuel Augusto, ya sallami babban daraktan harkokin Afirka, Gabas ta tsakiya da kungiyoyin kasashen yankin a ma'aikatar harkokin wajen Joaquim do Espírito Santo da kuma mukaddashin jakadan Angolan a ofishin jakadancin kasar a HKI, João Diogo Fortunato saboda halartar bikin bude ofishin jakadancin Amurka a birnin Qudus da mukaddashin jakadan yayi.
-
Zimbabwe : Majalisa Za Ta Saurari Mugabe Kan Batan Kudadin Lu'u-Lu'u
May 23, 2018 01:20A Zimbabwe, yau Laraba ne ake sa ran kwamitin majalisar dokokin kasar mai kula da harkokin ma'adunai da makamashi, zai saurari tsohon shugaban kasar Robert Bugabe kan badakalar salwantar wasu kudaden rara na lu'u-lu'u da yawansu ya kai Dalar Amurka Bilyan 15.
-
Burundi : An Yi Na'am Da Yi Wa Kundin Tsarin Mulki Kwaskwarima
May 21, 2018 12:49A Burundi, sakamakon zaben raba gardama da aka kada kuri'arsa ya nuna cewa mafi yawan 'yan kasar sun amince da aka yi wa kundin tsarin mulkin kasar kwaskwarima.
-
An Yi Gargadi Kan Tasirin Gwamnatin H.K. Isra'ila A Nahiyar Afrika
May 19, 2018 07:30Wani dan jarida kuma tsohon dan Majalisar Dokoki a kasar Tunusiya ya yi gargadi kan tasirin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila a nahiyar Afrika.
-
WHO : Annobar Ebola Bata Kai Matsayin Barazana Ga Duniya Ba
May 19, 2018 01:00Hukumar lafiya ta duniya WHO, ta ce annobar cutar Ebola data bulla a Jamhuriya Demokuraddiyar Congo, bata kai matsayin babbar barazana ga duniya ba, kasancewar ana da halin murkushe cutar ta hanyar matakan da aka dauka wandanda suka hada da allurar riga kafi.
-
Nijar : An Fara Sauraren Jagororin Kungiyoyin Fara Hula Da Ake Tsare Da
May 15, 2018 01:18A Jamhuriya Nijar, an fara sauraren jagororin kungiyoyin fara hular nan da ake tsare da a gidajen kurkuku kan bijirewa dokar hana zanga zanga a ranar 25 ga watan Maris da ya gabata.
-
OCHA : Ambaliyar Ruwa Ta Raba Mutane 220,000 Da Muhallansu A Somaliya
May 13, 2018 13:34Ofishin kula da harkokin jin kai na MDD ya bayyana cewa, kimanin mutane dubu dari biyu da ashiri ne, suka rasa matsugunansu, sakamakon barnar da kogunan Juba da Shabelle ke ci gaba da yi bayan da suka tumbatsa biyo bayan ruwan sama mai karfin gaske da aka tabka.
-
Korar 'Yan Gudun Hijira Sudan Daga Nijar, Rashin Imani Ne_Amnesty
May 13, 2018 10:04Kungiyar kare hakkin bil adama ta kasa da kasa (Amnesty International), ta yi tir da matakin hukumomin Nijar na korar 'yan Sudan dake neman mafaka a kasar.
-
Mutum Guda Ya Mutu Wasu Sun Sami Raunuka Wajen Rantsar Da Sabon Shugaban Saliyo
May 13, 2018 01:02Rahotanni daga kasar Saliyo sun ce alal akalla mutum guda ya mutu kana wasu kimanin 20 kuma sun sami raunuka a lokacin da suke kokarin kutsawa cikin babban filin wasan kwallon kafa na garin Freetown, babban birnin kasar don halartar bikin rantsar da sabon shugaban kasar Julius Maada Bio a jiya Asabar.
-
DRC : Adadin Mutanen Da Suka Kamu Da Cutar Ebola Ya Kai 11
May 11, 2018 01:23Hukumomin kiwan lafiya a Jamhuriya Demokuradiyyar Kango sun ce adadin mutanen da aka tabbatar sun kamu da cutar Ebola a kasar ya karu zuwa goma sha daya.