-
WHO: Za'a Fara Gwajin Rigakafin Cutar Malaria A Wasu Kasashen Afirka
Apr 24, 2017 12:43Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta sanar da cewa za ta fara gwajin rigakafin cutar zazzabin cizon sauro (malaria) a kasashe uku na Afirka da suka hada da kasashen Ghana, Kenya da kuma Malawi.
-
Kasar Habasha Ta Sanar Da Kame Wasu 'Yan Tawayen Da Suke Samun Goyon Bayan Eritrea
Apr 22, 2017 01:14Jami'an tsaron kasar Habasha (Ethiopia) sun sanar da kama wasu mutane 98 da gwamnatin ta kira da masu neman tada tsaye a kasar da suke samun goyon bayan kasar Eritrea a jiya Juma'a.
-
Mauritania : Za'a Je Zaben Raba Gardama
Apr 21, 2017 13:15A Mauritaniya za'a gudanar da zaben jin ra'ayin al'ummar a ranar 15 ga watan Yuli mai zuwa game da kudirin gwamnatin kasar na aiwatar da wasu sauye-sauye a kundin tsarin mulkin kasar.
-
Rahotanni: Sama Da Mutane 600 Sun Mutu Yayin Zanga-Zanga A Kasar Ethiopia
Apr 19, 2017 06:45Kungiyoyin kare hakkokin bil'adama na kasar Ethiopia sun bayyana cewar sama da mutane 600 ne suka rasa rayukansu sakamakon zanga-zangogin kin jinin gwamnatin kasar da aka ta gudanarwa a shekarar da ta gabata.
-
Wasu 'Yan Bindiga Sun Harbe Jami'an 'Yan Sanda 8 A Tanzania
Apr 14, 2017 10:51Wasu masu dauke da makamai sun harbe jami'an 'yan sanda 8 a gabashin kasar Tanzania.
-
Afrika Ta Tsakiya : Amurka Ta Kakabawa Jagororin Mayaka Takunkumi
Apr 13, 2017 01:24Amurka ta sanar da kakabawa shugabanin mayakan dake rikici a jamhuriya Afrika ta tsakiya takunkubi saboda hannun da suke da shi a rkicin da kasar ta tsunduma.
-
ICC Za Ta Saurari Afrika Ta Kudu Kan Kin cafke Al-Bashir
Apr 07, 2017 00:05Yau Juma'a ne ake sa ran kotun hukunta mayan laifuka ta duniya za ta saurari gwamnatin Afrika ta Kudu kan kin cafke shugaba Omar Al-Bashir na Sudan da take zargi da laifin kisan kare dangi.
-
Mali: An kawo Karshen Taron Kasa Na Sasanta Al'ummu
Apr 04, 2017 12:27A jiya litinin ne aka kawo karshen taron sasanta al'ummu a birnin Bamaku tare da cimma matsaya akan batun Azwad.
-
Sudan: An Bude Taro Akan Harkokin Tsaro A Nahiyar Afirka Da Kasashe 30 Su ke Halarta.
Apr 04, 2017 12:25Jami'an tsaro daga kasashe 30 na nahiyar Afirka sun fara zaman kwanaki uku domin tattauna barazanar ta'addanci da nahiyar ta ke fuskanta.
-
Shugabannin Wasu Kabilun Libya Sun Sanya Hannu A Kan Yarjejeniyar Sulhu
Apr 02, 2017 13:19Manyan kabilun kudancin kasar Libya sun sanya hannu a kan wata yarjejeniyar sulhu a birnin Rom na kasar Italiya.