-
Shugaban Ghana Ya Kare Shirin Gwamnatinsa Na Barin Amurka Ta Jibge Sojojinta A Kasar
Apr 07, 2018 11:19Shugaban kasar Ghana Nana Akufo-Addo ya kare matsayar gwamnatinsa na amincewa da shirin gwamnatin Amurka na jibge sojojinta a kasar Ghanan, yana mai cewa hakan zai kara karfafa shirin tsaro da zaman lafiya a yankin Yammacin Afirka.
-
Shugaban Iraki Ya Ki Amincewa Da Zaman Sojojin Amurka Na Har Abada A Kasar
Apr 07, 2018 11:18Shugaban kasar Iraki Fuad Masum ya bayyana cewar har ya zuwa yanzu ba a yanke shawarar barin Amurka ta kafa sansanin sojojinta na dindindin a kasar Irakin ba, yana mai cewa gwamnatin Iraki ba za ta taba bari a mai da kasar ta zamanto wani waje da za a kai wa wata kasa ta makwabta hari ba.
-
Amurka Ta Kakaba Wa Wasu Jami'an Rasha 38 Takunkumi
Apr 06, 2018 17:35Ma'aikatar baitalmalin Amurka, ta sanar da kakaba wa wasu jami'an Rasha su 38 takunkumi, ciki har da wasu makusanta shugaban Rashar Vladimir Putin.
-
Trump Na Tunanin Janye Sojojin Amurka Daga Siriya
Apr 04, 2018 11:17Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya bayyana cewa Amurka za ta yanke shawara game da janye sojojinta a yankin gabas ta tsakiya ko kuma akasin haka nan bada dadewa ba.
-
Trump Ya Yi Barazanar Korar Bakin Haure Kimanin Dubu Biyu
Apr 02, 2018 06:27Shugaban kasar Amurka ya dage tsugunar da 'yan gudun hijra kimanin miliyan daya da dubu dari takwas tare da bukatar daukan tsauraren matakai na kare iyakokin kasar.
-
Amurka Ta Bai Wa HKK Damar Ci Gaba Da Kashe Palasdinawa.
Apr 01, 2018 06:37Amurka Ta Bai Wa HKK Damar Ci Gaba Da Kashe Palasdinawa.
-
Dubban 'Yan Kasar Ghana Na Zanga-Zangar Kin Amincewa Da Jibge Sojojin Amurka A Kasar
Mar 28, 2018 16:11Dubun dubatan al'ummar kasar Ghana ne suka gudanar da wata zanga-zanga a birnin Accra, babban birnin kasar, don nuna rashin amincewarsu da yarjejeniyar fadada alaka ta soji tsakanin kasar Ghanan da kasar Amurka lamarin da zai ba wa Amurkan damar jibge sojojinta a kasar Ghanan.
-
An Samu Rarrabuwan Kai A Kasar Ghana Dangane Da Izinin Jibge Sojojin Amurka A Kasar
Mar 24, 2018 16:59A samu rarrabuwan kai tsakanin 'yan majalisar kasar Ghana da al'ummar kasar bayan da majalisar ta amince da bai wa Amurka damar girke sojojinta da kuma makamansu a kasar, bayan da ‘yan adawan suka kauracewa zaman majalisar yayin kada kuri'ar.
-
Kasar Amurka Ta Yi Barazanar Ficewa Daga Kwamitin Kolin Kare Hakkin Bil-Adama Na MDD
Mar 24, 2018 06:26Jakadiyar kasar Amurka a Majalisar Dinkin Duniya ta yi barazanar cewa: Amurka zata fice daga cikin kwamitin kolin kare hakkin bil-Adama na Majalisar Dinkin Duiniya matukar kwamitin ya ci gaba da fitar da kuduri kan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra'ila.
-
Amurka Ta Dage Haraji Kan Karafa Ga Abokan Huldarta
Mar 23, 2018 05:52Shugaba Donald Trump na Amurka ya bada umurnin dage haraji kan karafa da dalma ga kasashen da ya kira abokan huldar kasarsa masu mahimmanci ciki har da tarayya turai.