-
Sudan Ta Musunta Zargin Amurka Kan kare Hakkin bil Adama
Jan 22, 2018 11:16Kasar Sudan ta musunta zargin da Amurka ta yi mata dangane da kare hakkokin bil Adama.
-
Sabuwar Siyasar Tsaron Kasar Amurka Da Zargi Maras Tushe Kan Kasar Iran
Jan 21, 2018 06:45A ranar Juma'ar da ta gabata ce sakataren tsaron kasar Amurka Jim Mattis ya gabatar da abin da suke kira "Dabarun Tsaron Kasar Amurka Na Shekara ta 2018", inda ya bayyana kasashen Rasha Da China a matsayin babbar barazana ga Amurka da kawayenta a fage na kasa da kasa, sannan a yankin Gabas ta tsakiya da Asiya kuma ya bayyana Iran da Koriya ta Arewa a matsayin manyan kalubalen da Amurkan take fuskanta a yankin.
-
Bincike Ya Nuna Cewa Fiye Da Kashi 90% Na Makaman Nukliya A Duniya Na Hannun Amurka Da Rasha
Jan 20, 2018 06:14Wata cibiyar bincike mai rajin kawo sulhu da zaman lafiya a duniya dake birnin Stolkhom na kasar Sweden ce ta bayyana hakan.
-
Sayyid Hasan Nasrullahi Ya Bukaci Kasashen Musulmi Da Su Nisanci Kulla Alaka Da H.K.Isra'ila
Jan 19, 2018 19:01Babban sakataren kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullahi da ke kasar Lebanon ya bukaci kasashen musulmi da su nisanci kulla alakar jakadanci da Haramtacciyar kasar Isra'ila.
-
Jakadan Equatorial Guinea A MDD Ya Soki Amurka Kan Rashin Neman Gafarar Kasashen Afrika
Jan 19, 2018 18:22Jakadan kasar Equatorial Guinea a Majalisar Dinkin Duniya ya yi kakkausar suka kan kasar Amurka saboda rashin neman gafarar kasashen nahiyar Afrika dangane da maganganun cin zarafi da batanci da shugaban Amurka Donald Trump ya yi kan kasashen na Afrika.
-
Gwamnatin Nigeria Ta Kira Jakadan Amurka A Kasar Don Nuna Bacin Ranta Kan furucin Trump
Jan 16, 2018 06:34Ma'aikatar harkokin wajen tarayyar Nigeria a Abuja ta kira mataimakin jakadan Amurka a kasar David Young, zuwa gaban ministan harkokin wajen kasar Geoffrey Onyeama don samun karin bayani kan furucin wulakanci wanda shugaban kasar Amurka ya yi kan kasashen Afrika.
-
Iran Ba Za Ta Girmama Wani Abu Sama Da Abin Da Aka Cimma A Yarjejeniyar Nukiliya Ba
Jan 13, 2018 17:06Ma'aikatar harkokin wajen kasar Iran ta bayyana cewar Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba za ta girmama duk wani abu sama da abin da aka cimma a yarjejeniyar nukiliyar da ta cimma da manyan kasashen duniya a shekara ta 2015 ba.
-
Ministan Tsaron Iran Ya Ce Amurka Za Ta Fuskanci Mai Da Martani Daga Iran
Jan 10, 2018 11:23Ministan tsaron kasar Iran Birgediya Janar Amir Hatami ya bayyana cewar Amurka za ta fuskanci kakkausar mai da martani saboda hasarorin da ta janyo wa Iran sakamakon fitinar baya-bayan nan kamar yadda ta fuskanta a dukkanin fitinar da ta haifar a Iran.
-
Ravanchi: Idan Amurka Ta Fice Daga Yarjejjeniyar Nukiliyar Iran Za Ta Cutu Sama Da Iran
Jan 10, 2018 06:25Shugaban Ofishin Siyasa na Shugaban kasar Jamhuriyar musulinci ta Iran ya ce shakka babu idan Amurka ta fice daga yarjejjeniyar da Iran ta cimma kan shirinta na nukiliya na zaman lafiya za ta yi nadama kuma za ta cutu fiye da kasar Iran.
-
An Zargi Amurka Da Hannu A Tashe-tashen Hankula A Iran
Jan 09, 2018 19:13Wani tsohon jami'in Baitulmalin Amurka, -Paul Craig Roberts ne ya tabbatar da cewa kasarsa tana da hannu a cikin tashe-tashen hankulan da suka faru a Iran a makwannin da suka gabata.