An Zargi Amurka Da Hannu A Tashe-tashen Hankula A Iran
https://parstoday.ir/ha/news/middle_east-i27151-an_zargi_amurka_da_hannu_a_tashe_tashen_hankula_a_iran
Wani tsohon jami'in Baitulmalin Amurka, -Paul Craig Roberts ne ya tabbatar da cewa kasarsa tana da hannu a cikin tashe-tashen hankulan da suka faru a Iran a makwannin da suka gabata.
(last modified 2018-08-22T07:01:16+00:00 )
Jan 09, 2018 15:43 UTC
  • An Zargi Amurka Da Hannu A Tashe-tashen Hankula A Iran

Wani tsohon jami'in Baitulmalin Amurka, -Paul Craig Roberts ne ya tabbatar da cewa kasarsa tana da hannu a cikin tashe-tashen hankulan da suka faru a Iran a makwannin da suka gabata.

-Paul Craig Roberts ya  rubuta a shafinsa na internet cewa; A wani jikon  Washington ta sake bude rikici da al'ummar Iran.

-Paul Craig Roberts ya ci gaba da cewa; Tun bayan juyin musulunci na Iran Amurka take tsoma bakinta a harkokin cikin gidan Iran tare da yin barna.

Bayan abinda ya faru a Iran, din kasar Amurka ta kira yi taron gaggawa na kwamitin tsaron Majalisar Dinkin Duniya akan Iran, sai dai zaman ya kare da mai da Amurkan saniyar ware.