-
An hallaka 'yan ta'adda da dama a Najeria
Mar 28, 2016 11:43Dakarun Tsaron Najeria Sun hallaka Mayakan Boko Haram da dama A jihar Borno
-
Najeriya : An Tabbatar da Sace Soja
Mar 28, 2016 01:21Hukumomin sojin Nijeriya sun bayyana a Lahadi nan cewa, wasu dauke da makamai da ba a san ko su wane ne ba sun yi garkuwa da wani babban jami'in soji na kasar a jihar Kaduna da ke arewacin kasar.
-
Buhari Ya Taya Mutanen Da Gobarar Kasuwanni Kano Da Kebbi Ta Ritsa Da Su Jaje
Mar 27, 2016 10:55Shugaba Muhammadu Buhari na Nijeriya ya bayyana alhini da kuma juyayinsa dangane da gobarar da ta faru a kasuwar sabon gari da ke jihar Kano da kuma ta babbar kasuwar birnin Kebbi ta jihar Kebbi inda ya kirayi gwamnatocin jihohin biyu da su dau matakan da suka dace wajen hana sake faruwar hakan.
-
Nijeriya Za Ta Tura Iyayen 'Yan Matan Chibok Kamaru Don Tantance 'Yan Kunar Kakin Wake
Mar 27, 2016 10:36Gwamnatin Nijeriya ta sanar da aniyarta ta tura wasu daga cikin iyaye da mutanen garin Chibok da a baya 'yan kungiyar Boko Haram suka sace wasu 'yan mata 'yan makaranta a garin zuwa kasar Kamaru domin tantance ko wata 'yar kunar bakin waken da aka kama a can din tana daga cikin 'yan matan Chibok da aka sace kamar yadda ta yi ikirari.
-
Ma'aikata A Jahar Kaduna Sun Ce Suna Tare Da NLC
Mar 25, 2016 13:32Ma'aikata a jahar Kaduna sun ce suna tare da kungiyar kwadago ta kasa daram, babu wanda zai iya raba su da ita, kamar yadda za a ji a cikin wannan rahoto.
-
Yan Kungiyar Boko Haram Sun Sace Mata Ciki Har Da Budurwaye A Jihar Adamawan Nigeriya
Mar 25, 2016 06:07Yan kungiyar Boko Haram sun sace wasu mata 16 ciki har da budurwaye biyu a jihar Adamawa da ke arewacin tarayyar Nigeriya.
-
Sojojin Nigeria Sun Kwato Garin Kala Balge Daga Hannun Boko Haram
Mar 24, 2016 23:59Rundunar sojan Nijeriya ta sanar da fatattakan 'yan kungiyar Boko Haram daga garin Kala Balge da ke jihar Borno da kuma kwace ikon garin daga hannun, bugu da kari kan kubutar da mutane kimanin 520 da suke hannun 'yan ta'addan.
-
Helkwatar Sojin Nijeriya Ta Mayar Da Martani Ga Sabon Faifan Bidiyon Shekau
Mar 24, 2016 23:32Helkwatar tsaron Nijeriya ta yi watsi da sabon faifai bidiyon da shugaban kungiyar Boko Haram Abubakar Shekau ya fitar inda ta ce za ta ci gaba da kai hare-haren da take kai wa 'yan kungiyar da nufin ganin bayansu duk kuwa da halin damuwar da Shekau din ya nuna yana ciki a sabon faifan bidiyon.
-
'Yan Sandan Taraba Sun Tabbatar Da Kama Kwamandojin Boko Haram 2
Mar 24, 2016 04:49Rundunar 'yan sandan jihar Taraba a Nijeriya ta tabbatar da kama wasu kwamandojin kungiyar Boko Haram guda 2 wadanda aka jima ana nemansu inda ta ce tuni ta mika su ga sojoji a jihar.
-
Najeriya: Majalisar Dattijai Ta Amince Da Kasafin Kudin 2016
Mar 23, 2016 14:44Majalisar dattijan Najeriya ta amince da kasafin kudin da shugaba Buhari ya gabatar mata na shekara ta 2016.