-
Shugaba Jammeh Ya Ce Zai Ci Gaba Da Mulki Har Sai Kotun Koli Ta Yanke Hukumcin Karar Da Ya Shigar
Jan 12, 2017 05:34ِDuk da kiraye-kirayen da ake masa na ya sauka daga karagar mulki, shugaban kasar Gambia Yahya Jammeh ya sha alwashin ci gaba da zama zama a kan kujerar mulki har sai kotun kolin kasar ta yanke hukunci dangane da karar da ya shigar inda yake kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasar da aka sanar cewa ya sha kaye.
-
Sojoji Sun Bar Hedikwatar Hukumar Zaben Kasar Gambiya
Dec 30, 2016 10:29Rahotanni daga kasar Gambiya sun bayyana cewar sojojin kasar sun bar hedikwatar hukumar zaben kasar bayan mamaye wajen da suka yi na sama da makonni biyu da kuma korar ma'aikatan da suke wajen.
-
'Yan Adawan Gambiya: Jammeh Zai Zamanto Dan Tawaye Matukar Bai Mika Mulki A 19 Ga Janairu Ba
Dec 29, 2016 11:52Hadin gwiwan jam'iyyun 'yan adawan kasar Gambiya sun bayyana cewar shugaban kasar Yahya Jammeh zai zamanto dan tawaye daga 19 ga watan Janairu matukar dai bai mika mulki a wannan ranar ga zababben shugaban kasar Adama Barrow ba.
-
Adama Barrow Ya Kirayi Yahya Jammeh Da Ya Mika Mulki Cikin Ruwan Sanyi
Dec 27, 2016 17:37Zababben shugaban kasar Gambia mai jiran gado Adama Barrow ya kirayi shugaban kasar mai barin gado wanda kuma ya sha kayi a zabe Yahya Jammeh, da ya girmama sakamakon zaben kuma ya mika mulki ta hanyar ruwan sanyi.
-
'Yan Adawar Gambiya: Babu Wata Kotu Da Za Ta Soke Zaben Adamar Barrow Da Aka Yi
Dec 24, 2016 16:48Gamayyar 'yan adawan kasar Gambiya sun yi watsi da sanarwar da kotun kolin kasar ta yi na fara sauraran karar da shugaban kasar Yahya Jammeh ya shigar yana kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasar inda suka ce babu wata kotu a duniyar nan da ta isa ta sauya nasarar da dan takararsu Adamar Barrow ya samu a zaben 1 ga watan Disamban da aka gudanar.
-
Amsar Jammeh Ga ECOWAS: Ba Zan Sauka Daga Karagar Mulki Ba
Dec 22, 2016 05:50Shugaban Gambiya Yahya Jammeh ya yi watsi da kokarin da shugabannin kungiyar tattalin arziki na Yammacin Afirka (ECOWAS) suke yi na sasanta rikicin siyasar kasar, yana mai cewa babu abin da zai sa shi sauka daga karagar mulkin kasar.
-
Kungiyar OIC Ta Bukaci Shugaba Jammeh Da Ya Sauka Daga Mulki Don Gudun Rikici
Dec 16, 2016 17:13Kungiyar Hadin Kan Kasashen Musulmi (OIC) ta bukaci shugaban kasar Gambiya Yahya Jammeh da ya girmama sakamakon zaben 1 ga watan Disamban da aka gudanar a kasar inda aka sanar da Adama Barrow a matsayin wanda ya lashe zaben.
-
Jam'iyyar Shugaba Jammeh Ta Shigar Da Kara Kan Sakamakon Zaben Shugaban Kasar
Dec 14, 2016 11:07A daidai lokacin da alamu suke nuni da rashin nasarar kokarin shiga tsakanin da kungiyar ECOWAS ta tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka take yi don magance rikicin siyasar da ya kunno kai a kasar Gambiya, jam'iyyar APRC mai mulki a kasar ta shigar da kara tana kalubalantar sakamakon zaben shugaban kasar da hukumar zaben kasar ta sanar inda ta ce shugaba Yahya Jammeh ya sha kaye.
-
Shugaban Hukumar Zaben Gambiya Ya Ja Kunnen Shugaba Jammeh
Dec 13, 2016 11:11Shugaban hukumar zaben kasar Gambiya Alieu Momarr Njai ya ja kunnen shugaban kasar Yahya Jammeh dangane da kin amincewa da sakamakon zaben shugaban da yayi yana mai cewa hakan ba zai sauya hakikanin lamarin cewa ya sha kaye a zaben shugaban kasar da aka gudanar ba.
-
An tabka Magudi a zaben Gambia
Dec 12, 2016 05:21Jam'iya mai millki ta kasar Gambia ta zarki Kwamitin zabe da tabka magudi a zaben shugaban kasa.