-
'Yan Majalisar Pakistan Sun Yi Watsi Da Shirin Gwamnatin Kasar Na Tura Sojoji Saudiyya
Feb 17, 2018 11:19'Yan majalisar dokokin kasar Pakistan sun yi watsi da matakin da gwamnatin kasar ta dauka na tura sojoji zuwa kasar Saudiyya suna masu cewa hakan ya saba wa kudurin da Majalisar ta fitar da ta bukaci gwamnatin ta ci gaba da zama 'yar ba ruwanmu dangane da yakin da Saudiyyan ta kaddamar kan kasar Yemen.
-
Pakistan Ta Kori 'Yan Gudun Hijira Afganistan Milyan Biyu
Feb 03, 2018 06:30A daidai lokacin da dangantaka ke kara tsami tsakanin kasashen Afganistan da Pakistan, hukumomin Islamabad sun kara matsa kaimi wajen korar 'yan gudun hijira Afganistan.
-
Pakistan : Harin Kunar Bakin Wake Ya kashe Mutum 5 A Coci
Dec 17, 2017 11:11Rahotanni daga Pakistan na cewa mutane a kalla biyar ne suka gamu da ajalinsu a wani harin kunar bakin wake a wani coci dake kudu maso yammacin kasar.
-
Ministan Shari'a Na Pakistan Ya Yi Murabus
Nov 27, 2017 06:33Minsitan shari'a na kasar Pakistan, Zahid Hamid, ya mika takardar murabus dinsa ga firayi ministan kasar Shahid Khaqan Abbasi.
-
Pakistan : An Fitar Da Sammacin Kame Nawaz Sharif
Oct 26, 2017 11:21Kotun da ke kula da yaki da cin hanci da rashawa a Pakistan, ta bayar da sammacin kame tsohon firayi ministan kasar, Nawaz Sharif, bisa badakalar cin hanci da rashawa.
-
Gobara Ta Yi Ajalin Mutum 47 A Indonesia
Oct 26, 2017 11:21Rahotanni daga Indonesia, na cewa mutane a kalla 47 ne suka gamu da ajalinsu a wata mummunar gobar da ta auku a wani kamfanin safara ababen wasan wuta a wajen Jakarta babban birnin kasar.
-
Taliban Ta Kai Mummunan Hari A Wani Barikin Sojin Afganistan
Oct 19, 2017 18:07Kungiyar Taliban na ci gaba da zazzafa kai hare harenta kan sojojin kasar Afganistan, inda ta kai hare hare guda uku a cikin sa'o'i 48 da suka gabata.
-
Manyan Hafsoshin Sojojin Iran Da Pakistan Sun Yi Kiran Da A Taimaka Wa Musulmin Rohingya
Sep 17, 2017 16:54Manyan hafsoshin sojojin Iran da Pakistan sun bukaci kasashen duniya da su dau matakan da suka dace kuma na hakika wajen kawo karshen kisan kiyashin da ake yi wa musulmin Rohingya na kasar Myammar.
-
Shugaba Ruhani: Kasashen G/Tsakiya Ne Kawai Za Su Iya Tabbatar Da Tsaron Yankin
Sep 11, 2017 17:51Shugaban kasar Iran Dakta Hasan Ruhani yayi kakkausar suka ga irin tsoma bakin da manyan kasashen duniya suke yi cikin harkokin cikin gidan kasashen yankin Gabas ta tsakiya yana mai cewa kasashen yankin ne kawai za su iya tabbatar da tsaronsa.
-
Pakistan : An Zabi Shahid Khaqan Abbasi A Matsayin Sabon Firaminista
Aug 01, 2017 16:46Majalisar dokoki a Pakistan ta zabi Shahid Khaqan Abbasi a matsayin sabon Firaminista bayan kotun kolin kasar ta tube Nawaz Sharif kan badakalar rashawa a makon jiya.