-
Sudan ta kudu ta soki Gwamnatin Kwango a kan fitar da Riek Machar daga cikin kasar
Aug 29, 2016 10:30Ministan Sadarwa na kasar Sudan ta kudu ya ce abinda Kasar Demokaradiyar Kwango ta yi na fitar da Riek Machar daga cikin kasar ya sabawa dokokin kasa da kasa
-
An Sallami Magudun 'Yan Tawayen Sudan Ta Kudu Daga Asibiti A Kasar Sudan
Aug 26, 2016 12:30Rahotanni daga kasar Sudan bayyana cewar an sallami madugun 'yan tawayen kasar Sudan ta Kudu Riek Machar daga asibitin da yake kwance a can a kasar Sudan din sai dai kuma zai ci gaba da zama a birnin Khartoum, babban birnin kasar Sudan din har zuwa wani lokaci don kara murmurrewa.
-
Yarjejjeniyar Sudan da Sudan ta Kudu kan sake buda iyakokin kasashen biyu
Aug 25, 2016 02:18Kasar Sudan da Sudan ta kudu sun cimma matsaya a kan sake buda iyakokin kasashen biyu.
-
Kasashen Sudan Biyu Sun Amince A Bude Kan Iyakokinsu
Aug 24, 2016 07:47Jami'an gwamnatocin Kasashen Sudan da Sudan ta Kudu sun cimma yarjejeniyar Bude kan iyakokinsu Biyu
-
MDD Ta Nada Jami'in Bincike Mai Cin Gashin Kansa Kan Rikicin Kasar Sudan Ta Kudu
Aug 24, 2016 00:42Babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki Moon ya sanar da nada tsohon sojan kasar Holland Manjo Janar patrick Cammaert a matsayin jami'i mai gudanar da bincike kan rikicin da ya faru a birnin Juba, babban birnin kasar Sudan ta Kudu a watan Yulin da ya gabata lamarin da ya sake janyo rikici da zaman dardar na siyasa a kasar.
-
Sabon Mataimakin Sudan Ta Kudu Ya Fara Ziyarar Aiki A Khartum
Aug 21, 2016 13:12Mataimakin shugaban kasar Sudan ta kudu Taban Deng Gai ya fara gudanar da wata ziyarar aiki ta kwanaki biyu a jamhuriyar Sudan, inda ya isa birnin Khartum a yau.
-
Asusun Kula Da Kananan Yara Na M.D.D Ya Nuna Damuwa Kan Mai Da Yara 'Yan Ta'adda A Sudan Ta Kudu
Aug 21, 2016 01:25Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya "UNICEF" ya bayyana cewa: Kananan yara fiye da dubu goma sha shida ne suka shiga cikin kungiyoyin 'yan bindiga a kasar Sudan ta Kudu musamman bayan bullar yakin basasa a kasar, inda a farkon wannan shekara zuwa yanzu yawan kananan yaran da suka shiga cikin kungiyoyi masu dauke da makamai suka haura 650.
-
Gargadin Asusun Kula Kananan Yara Na Majalisar Dinkin Duniya Kan Mai Da Kananan Yara 'Yan Ta'adda
Aug 19, 2016 12:51Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya {UNICEF} ya sanar da cewa: Kananan yara fiye da 650 ne kungiyoyin masu dauke da makamai a kasar SUdan ta Kudu suka kwasa domin horas da su a cikin wannan shekara ta 2016 da muke ciki.
-
Shugaban 'Yan Tawayen Sudan Ta Kudu Ya Isa Jamhuriyar Dimukradiyar Congo
Aug 19, 2016 01:21Jagoran 'yan tawayen Sudan ta kudu Reick Machar ya isa Jamhuriyar Dimukradiyyar Congo, bayan da ya bar kasar Sudan ta kudu sakamakon rikicin da ya kunno kai a tsakaninsa da shugaban kasar Salva Kiir.
-
Jan kunan Mataimakin Sudan ta Kudu ga Riek Machar
Aug 19, 2016 00:50Sabon Mataimakin Shugaban Sudan ta kudu ya galgadi Madugun 'yan tawayen kasar da ya bar kasar ta zauna lafiya