Kasashen Sudan Biyu Sun Amince A Bude Kan Iyakokinsu
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i10087-kasashen_sudan_biyu_sun_amince_a_bude_kan_iyakokinsu
Jami'an gwamnatocin Kasashen Sudan da Sudan ta Kudu sun cimma yarjejeniyar Bude kan iyakokinsu Biyu
(last modified 2018-08-22T06:58:49+00:00 )
Aug 24, 2016 07:47 UTC
  • Kasashen Sudan Biyu Sun Amince A Bude Kan Iyakokinsu

Jami'an gwamnatocin Kasashen Sudan da Sudan ta Kudu sun cimma yarjejeniyar Bude kan iyakokinsu Biyu

Jami'an gwamnatocin Kasashen  Sudan da Sudan ta Kudu sun cimma yarjejeniyar Bude kan iyakokinsu biyu.

Cimma yarjejeniyar a tsakanin kasashen biyu dai ya zo ne bayan ganawar da aka yi a tsakanin mataimakin shugaban kasar Sudan ta Kudu, Taban Dang Gai, da shugaba Umar Hassan al-Bashir a jiya litinin a birnin Khartom.

Bugu da kari, bangarorin biyu sun tattauna akan batutuwan da su ka shafi tsaro da kuma batun man fetur.

A gefe daya, kasar Sudan ta baiwa Sudan ta kudu tabbacin cewa ba za ta bada dama ga 'yan atwaye su sami matsugunni a cikin kasar ba.