Sabon Mataimakin Sudan Ta Kudu Ya Fara Ziyarar Aiki A Khartum
https://parstoday.ir/ha/news/africa-i9952-sabon_mataimakin_sudan_ta_kudu_ya_fara_ziyarar_aiki_a_khartum
Mataimakin shugaban kasar Sudan ta kudu Taban Deng Gai ya fara gudanar da wata ziyarar aiki ta kwanaki biyu a jamhuriyar Sudan, inda ya isa birnin Khartum a yau.
(last modified 2018-08-22T06:58:48+00:00 )
Aug 21, 2016 13:12 UTC
  • Sabon Mataimakin Sudan Ta Kudu Ya Fara Ziyarar Aiki A Khartum

Mataimakin shugaban kasar Sudan ta kudu Taban Deng Gai ya fara gudanar da wata ziyarar aiki ta kwanaki biyu a jamhuriyar Sudan, inda ya isa birnin Khartum a yau.

Karamin ministan harkokin waje na kasa Sudan Kamaluddin Isma'il ya fadi yau cewa, Taban Deng zai gana da manyan jami'an gwamnatin Sudan da suka hada da shugaba Umar Hassan Albashir, a kan batutuwa da suka shafi alaka a tsakanin kasashen biyu.

Shugaban kasar Sudan ta kudu ya nada Taban Deng Gai a matsayin mataimakinsa ne biyo bayan rikciin da ya barke tsakanin magoya bayansa da kuma magoya bayan Reik Machar madugun 'yan tawaye, wanda ya dawo Juba a matsayin mataimakin shugaban kasa bayan yarjejeniyar sulhu da aka cimmawa, sai kungiyar kasashen gabashin Afirka IGAD ta ce ba ta amince da nada Taban Deng a matsayin mataimakin shugaban kasar Sudan ta kudu ba.