• Ana Dakon Sakamakon Zaben Shugaban Kasa A Angola

    Ana Dakon Sakamakon Zaben Shugaban Kasa A Angola

    Aug 24, 2017 10:21

    Al'umma a Angola na ci gaba da dakon sakamakon zaben shugaban kasar da aka kada kuri'asa a jiya Laraba.

  • Yau Ne Za'a Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa A Kasar Angola

    Yau Ne Za'a Gudanar Da Zaben Shugaban Kasa A Kasar Angola

    Aug 23, 2017 00:55

    A yau ne ake sa ran al’ummar kasar Angola za su kada kuri’ar zaben 'yan majalisar kasar da zai share fagen zaben sabon shugaban kasar wanda zai maye gurbin shugaba Jose Eduardo Dos Santos wanda ya shafe kimanin shekaru 38 yana mulkin kasar.

  • WHO Ta Yi Gargadin Yaduwar Cututtuka A Saliyo

    WHO Ta Yi Gargadin Yaduwar Cututtuka A Saliyo

    Aug 22, 2017 06:27

    Hukumar lafiya ta duniya WHO, ta yi gargadin cewa, akwai yiwuwar yaduwar wasu cututtuka kamar amai da gudawa da zazzabin sauro a Saliyo, bayan iftiila'in ambaliyar ruwa da zaftarewar laka da ta auku a makon da ya gabata a kasar, wacce ta hadassa mutuwar mutane 500.

  • Sudan: Jam'iyyun Siyasar Kasashen Afirka Sun Yi Taro A Birnin Khartum.

    Sudan: Jam'iyyun Siyasar Kasashen Afirka Sun Yi Taro A Birnin Khartum.

    Aug 20, 2017 13:42

    Wakilan jam'iyyun siyasa 32 ne da su ka fito daga kasashen Afirka daban-daban su ka yi taron domin karfafa alakar aiki a tsakaninsu.

  • Sharhi:Kokarin HKI Na Samun Gindin Zama A Nahiyar Afirka

    Sharhi:Kokarin HKI Na Samun Gindin Zama A Nahiyar Afirka

    Aug 20, 2017 00:52

    A kokarinta na fita daga cikin halin kadaici, haramcecciyar kasar Isra'ila na kokarin fadada alakarta da kasashen nahiyar Afirka, dangane da wannan batu, magabatan birnin tel-aviv suka kudiri shirya wani taro mai taken zaman kasashen Afirka da Isra'ila cikin watan OKtoba mai zuwa a kasar Togo.

  • Ran-Gadin Shugaba Al'Sisi A Wasu Kasashen Afirka

    Ran-Gadin Shugaba Al'Sisi A Wasu Kasashen Afirka

    Aug 19, 2017 06:40

    A ci gaba da ran gadin da yake a wasu kasashen Afirka, shugaban kasar Masar Abdel Fattah Al-Sissi, ya gana da takwaransa na Chadi, Idriss Deby Itno jiya a birnin N’Djamena.

  • Mali : An Jingine Shirin Zaben Jin Ra'ayin Al'umma

    Mali : An Jingine Shirin Zaben Jin Ra'ayin Al'umma

    Aug 19, 2017 06:39

    Shugaban Ibrahim Bubakar Keita na Mali na sanar da dage shirin zaben jin ra'ayin al'ummar kasar kan yiwa kundin tsarin mulkin kasar kwaskwarima.

  • Nakiya Ta Kashe Sojojin Burkina Faso Uku

    Nakiya Ta Kashe Sojojin Burkina Faso Uku

    Aug 18, 2017 06:48

    Rahotanni daga Burkina faso na cewa sojojin kasar uku ne suka rasa rayukansu a yayin da motarsu ta taka nakiya a lardin Turonata dake karamar hukumar Tongomayel dake yankin Sahel a arewacin Wagadugu babban birnin kasar.

  • RD Congo : Zabtarewar Kasa Ta Yi Ajalin Mutum 40

    RD Congo : Zabtarewar Kasa Ta Yi Ajalin Mutum 40

    Aug 17, 2017 06:15

    Rahotanni daga Jamhuriya Demukuraddiyar Congo, na cewa mutane arba'in ne suka rasa rayukansu sakamakon zaftarewar kasa da aka samu a wani kauyen masinta a Ituri dake arewa maso gabashin kasa.

  • ICC : Dan Jihadi, Zai Biya Diyya A Timbuktu

    ICC : Dan Jihadi, Zai Biya Diyya A Timbuktu

    Aug 17, 2017 06:01

    Kotun hukunta mayan laifuka ta duniya cewa da ICC, ta ce dan jihadin nan na Mali Ahmad al Faqi al Mahdi zai biyan diyya ta Yuro miliyan biyu da dubu dari bakwaiu saboda lalata wurare masu tarihi a birnin Timbuktu.