-
Yawan 'Yan Gudun Hijira Sudan Ta Kudu Ya Kai Miliyan Guda A Uganda
Aug 17, 2017 04:29Hukumar kula da kaurar bakin haure ta MDD ta fitar da alkalumen dake cewa, yawan 'yan gudun hujira Sudan ta kudu a kasar Uganda ya kai miliyan guda.
-
Odinga Ya Ce Zai Daukaka Kara Kan Sakamakon Zaben Shugaban Kasar Kenya
Aug 17, 2017 01:08Jagoran ‘yan adawar kasar Kenya wanda kuma ya sha kaye a zaben shugaban kasar da aka gudanar Raila Odinga ya bayyana cewa zai daukaka kara a kotun koli ta kasar kan sakamakon zaben shugabancin kasar da aka sanar inda shugaba mai ci Uhuru Kenyatta ya lashe.
-
An Fara Zaman Makoki Na Mako Guda A Kasar Saliyo
Aug 16, 2017 14:47Gwamnatin kasar Saliyo ta sanar da zaman makoki na maku guda domin jimamin mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwa.
-
Ambaliyyar Ruwa Ta Yi Ajalin Mutum 312 A Saliyo
Aug 15, 2017 01:58Bayanai daga Saliyo na cewa a kalla mutane 312 ne suka rasa rayukansu a ibtila'in ambaliyar ruwa da zabtarewar kasa da laka data biyo bayan ruwan sama tamakar da bakin kwarya da aka samu a Freetown babban birnin kasar.
-
An Kashe Mutum 9 A Jerin Hare-hare Kan Sansanin MDD A Mali
Aug 15, 2017 01:57Rahotanni daga Mali na cewa mutane tara ne suka rasa rayukansu a wasu tagwayen hare-haren 'yan bindiga a sansanin tawagar kiyaye zaman lafiya ta MDD a Mali.
-
Fao: Gargadi Akan Fari A Gabacin Nahiyar Afirka
Aug 14, 2017 14:24Hukumar abinci ta duniya( fao) ta yi gargadi akan karuwar mutanen da suke mutuwa saboda fari a gabacin nahiyar Afirka.
-
Odinga Ya Ki Amincewa Da Shan Kaye, Yayi Kira Zuwa Ga Yajin Aiki
Aug 13, 2017 12:34Madugun 'yan adawan kasar Kenya Raila Odinga ya ki amincewa da kayen da ya sha a zaben shugaban kasar da aka gudanar yana mai kiran magoya bayansa da su fara yajin aiki don matsin lamba har sai an nada shi a matsayin shugaban kasa.
-
Ana Ci Gaba Da Dakon Sakamakon Zaben Shugaban Kasa A Kenya
Aug 11, 2017 13:43Al'ummar a Kenya na ci gaba da dakon sakamakon zaben shugaban kasar da aka kada kuri'arsa a ranar Talata data gabata.
-
Masar : Hadarin Jiragen Kasa Biyu Ya Yi Ajalin Mutum A kalla 36
Aug 11, 2017 11:06Hukumomin kiwon lafiya a Masar sun ce a kalla mutane 36 ne suka rasa rayukansu a yayin da wasu jiragen kasa biyu sukayi taho mu gama a arewacin kasar.
-
Nijar : Ana Bi Da Bakin Haure Ta Hanyoyi Masu Hadarin Gaske
Aug 09, 2017 02:01Hukumar kula da bakin haure ta MDD ta ce ana bin hanyoyi masu hadarin gaske da bakin haure a wani mataki na kaucewa matakan da hukumomi a NIjar suka dauka na hana safarar bakin hauren ta hamadar sahara.