WHO Ta Yi Gargadin Yaduwar Cututtuka A Saliyo
Hukumar lafiya ta duniya WHO, ta yi gargadin cewa, akwai yiwuwar yaduwar wasu cututtuka kamar amai da gudawa da zazzabin sauro a Saliyo, bayan iftiila'in ambaliyar ruwa da zaftarewar laka da ta auku a makon da ya gabata a kasar, wacce ta hadassa mutuwar mutane 500.
WHO ta kara da cewa, bisa la'akari da lalacewar hanyoyin ruwa da kayayyakin tsaftace muhalli, mazauna yankunan da iftila'in ya shafa a kasar dake yammacin Afrika na cikin hadarin fuskantar barkewar cututtukan.
Ko a shekarar 2012 ma dai an samu barkewar cuwar kwalara a kasar ta Saliyo.
A yanzu haka, WHO ta ce tana aiki da hukumomin lafiya na kasar ta Saliyo domin kara kaimi wajen daukar matakan kariya da kuma tunkarar barkewar cututtuka.