-
Ma'aikatar Kula Da Lamuran Addini A Masar Ta Hana Malaman Kasar Zuwa Iran
Jun 26, 2016 10:15Ma'aikatar kula da ayyukan addini a masar ta hana malaman addinin kasar zuwa Iran
-
Za a Tura Akwatin Nadar Bayanai na Jirgin Masar zuwa Faransa
Jun 24, 2016 09:42Kasar Masar Ta ce Za ta tura Akwatin Nadar Bayyanai na Jirgin Masar din da aka gano zuwa Kasar Faransa
-
'Yan Siyasar Masar Sun Yi Maraba Da Hukunci Soke Yarjejeniyar Mika Tsibirai Ga Saudiyya
Jun 22, 2016 11:44Rahotanni daga kasar Masar sun bayyana cewar da dama daga cikin kungiyoyi, jam'iyyu da 'yan siyasar kasar sun yi maraba da hukuncin da wata kotun kasar ta yanke na soke yarjejeniyar da gwamnatin kasar ta cimma da Saudiyya na mika mata ikon wasu tsibirai guda biyu na kasar.
-
Masar Ta Mayar Da Martani Ga Matsayar Qatar Kan Hukunci Da Aka Yanke Wa Morsi
Jun 20, 2016 06:33Ma'aikatar harkokin wajen kasar Masar ta mayar da martani ga gwamnatin kasar Qatar dangane da hukuncin da wata kotun kasar Masar ta yanke wa hambararren shugaban kasar Muhammad Morsi kan zargin da ake masa na leken asiri wa kasar Qatar din.
-
An yankewa Tsohon Shugaba Masar Hukuncin daurin rai da rai
Jun 18, 2016 10:54Kotu ta yankewa tsohon Shugaban kasar Masar Muhamad Morsi daurin rai da rai
-
Jami'ar Azhar Ta Gargadi Musulmi Kan Gurbatattun Akidu Da Ake Yawo Da Su
Jun 18, 2016 06:29Shugaban jami'ar al-Azhar ta kasar Masar, Sheikh Ahmad Tayyib ya bayyana cewar mutanen da suke dauke da gurbatattun akidu babbar barazana ce ga duniyar musulmi don haka ya kirayi musulmi da su yi taka tsantsan da irin wadannan mutanen.
-
An Gano Dukkan Akwatinan Nadar Bayannan Tukin Jirgin EgyptAir
Jun 18, 2016 01:20Kwamitin dake gudanar da bincike kan musababbin faduwar jirgin Egypt Air ya sanar da gano dukkan akwatinan nadar bayyanan tukin jirgin daya nutse a tekun Bahar-Rum a watan Jiya.
-
An Gano Wani Akwatin Nadar Bayannan Tukin Jirgin EgyptAir
Jun 16, 2016 09:50Kwamitin dake gudanar da bincike kan musababbin faduwar jirgin EgyptAir ya sanar da gano daya daga cikin akwatinan nadar bayyanan jirgin daya nutse a tekun Bahar-Rum a watan Jiya.
-
An Gano Wasu Tarkacen Jirgin EgyptAir
Jun 16, 2016 00:26An sake gano wasu daga cikin tarkacen jirgin nan na EgyptAir daya nutse a tekun Bahar-Rum a ranar 19 ga watan Jiya kamar yadda masu binciken musababin faduwar jirgin suka sanar.
-
Masar An Shigar Da Sunayen "Yan'uwa Musulmi Cikin Jerin 'yan ta'adda
Jun 15, 2016 14:35A kalla Sunayen mutane 215 na Kungiyar Ikhwanul-Muslimin Wata Kotu ta shigar cikin na 'yan ta'adda.