-
Jam’iyyar PDP ta kore Shugabanta na kasa Ali Modu Sheriff
May 21, 2016 14:37Rahotanni daga najeriya na cewa Jam’iyyar PDP ta kore Shugabanta na kasa Ali Modu Sheriff.
-
Buhari Ya Ba Da Umurnin Kara Tura Sojoji Yankin Niger Delta Don Fada Da Tsagera
May 21, 2016 00:40Shugaba Muhammadu Buhari na Nijeriya ya ce ya ba da umurnin kara tura sojoji yankin Niger-Delta don fada da 'yan tsageran yankin da suke ci gaba da kai hare-hare kan bututun mai da iskar gas lamarin da ke ci gaba da zagon kasa ga tattalin arzikin kasar da ke cikin mawuyacin hali.
-
Tsegerun Niger Delta Sun Kai Hari Kan Bubutun Man Fetur Na NNPC A Yankin
May 20, 2016 13:21Tsagerin Niger Delta a tarayyar Nigeria sun kai hare hare kan bututan man fetur na kamfanin NNPC a yankin
-
An sake fasa wani bututun Gaz a yankin Niger-Dalta a Najeria
May 19, 2016 12:53Tsagerun Niger-Dalta sun sake fasa wani bututun iskar Gaz na kamfanin ENI mallakin kasar Italiya a yankin.
-
Fadar Shugaban Nijeriya: 'Yar Chibok Za Ta Gana Da Buhari A Yau Alhamis
May 19, 2016 00:57Fadar shugaban Nijeriya ta sanar da cewa a yau Alhamis, shugaba Muhammadu Buhari zai gana da daya daga cikin 'yan matan Chibok din nan da aka kwato daga hannun Boko Haram, a daidai lokacin da ake fatan za a samu bayanin da zai ga ceto sauran 'yan matan sama da 200 da Boko Haram din suka sace sama da shekaru biyu da suka wuce.
-
Rahotanni: Yajin Aikin Da NLC Ta Kira A Nijeriya Bai Yi Armashi Ba
May 19, 2016 00:56Rahotanni daga Nijeriya sun bayyana cewar yajin aikin da kungiyar kwadago ta kasar NLC ta kira a jiya Laraba don nuna rashin amincewa da karin farashin mai da gwamnatin tarayyar kasar ta yi bai yi armashi ba, sakamakon rarrabuwan kan da aka samu tsakanin shugabannin kwadagon.
-
Najeriya : An Samu Rabuwar Kawuna Kan Yajin Aiki
May 18, 2016 07:23A Najeriya an samu rabuwa kawuna gameda yajin aikin gama gari da mayan kungiyoyin kwadigo na kasar suka kira yau Laraba domin kalubalantar kara farashin man fetur da gwamnatin kasar tayi.
-
Kotu Ta Hana Kungiyoyin Kwadago Shiga Yajin Aiki A Nijeriya
May 17, 2016 13:30Kotun masana’antu a Nijeriya ta hana kungiyoyin kwadago ta kasar (NLC) da kuma ta 'yan kasuwa da masana'antu (TUC) fara yajin aikin da suka yi barazanar farawa a gobe Laraba.
-
EFCC Ta Kama Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Da Kuma Wani Na Kurkusa Da Jonathan
May 17, 2016 13:29Rahotanni daga Nijeriya suna bayyana cewar hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasar ta'annuti (EFCC) ta kama tsohon gwamnan jihar Kaduna, Ramalan Yero da kuma tsohon sakataren kashin kai na tsohon shugaban Nijeriya Goodluck Jonathan, Hasan Tukur bisa zargin sama da fadi na wasu makudan kudade.
-
An kame tsagerun Niger-Dalta masu fasa bututun Man A Najeriya
May 17, 2016 01:13Rundunar sojin Najeriya ta kama wasu daga cikin tsagerun Niger Delta da ke fasa bututun man fetir a yankinsu.